Gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin lnjiniya Abba Kabir Yusuf ta yi watsi da rahoton zargin rundunar Yan sanda na cewa ta Sami rahoton sirri na zargin da yuwawar batagari su kai hare-hare a wasu muhimman sansanin masu taron mauludin kasa.
Zargin da rundunar Yan sanda ta kasa reshen jihar Kano ta fitar a yammacin jiya juma’a ya ce akwai rahoton sirri da ya zo musu cewa akwi Yan taadda da suke Shirin Kai hare-hare a wasu muhimman sansanin masu taron mauludin.
Sai dai gwamnatin Kano ta bakin kwamishinan yada labarai da alamuran cikin gida Ibrahim Abdullahi Waiya, ta yi watsi da rahoton jamian tsaron.
Waiya da yake jawabi jiya afadar Mai martaba sarkin Kano Alh. Sanusi Lamido Sanusi ya baiyana matukar damuwar SA da rahoton jami’an tsaron.
Kana ya soki Shirin jami’an tsaro na rufe wuraren gudanar da taron mauludin da za’a yi wanda shine karo na 39
Ya Kara da cewa Kano jiha ce da ta yi shura wajen dabbaka alamuran addini da zaman lafiya da kwanciyar hankali.









