RelatedPosts
Daga Hassan Umar Gwammaja
Al’ummar Garin Kaibo Mada dake cikin Karamar Hukumar Keffi ta Jihar Nasarawa, sun zargi Sarakunan Bagaji da Masarautar Keffi da yunkurin kwace filaye da gonakin da suka ce sun gada a wurin iyaye da kakanni.
Hakan ce ta sanya suka fito mazan su da matan su domin gudanar da zanga-zangar lumana a titunan garin domin bayyana rashin jin dadinsu, inda suka yi zagaye dauke da kwalaye da ganye suna rera wakokin neman daukin Gwamnatin Jihar Nasarawa.
A cewar daya daga cikin masu zanga-zangar, Malam Salihu Musa, “Wannan filinmu ne da muka gada daga iyayenmu amma yanzu ana yunkurin kwace shi ba tare da wani dalili ba, adan haka muna kira ga Gwamna Injiniya Abdullahi Sule da ya sa baki cikin lamarin domin kare hakkokinmu”.
Ita ma wata dattijuwa me suna Hajiya Zainab Ibrahim, ta bayyana matuƙar damuwarta inda ta ce, “Idan aka kwace gonakinmu, to da me za mu ciyar da ‘ya’yanmu? Wannan ba adalci bane, kuma ba za mu yarda ba har sai mun ga gwamnati ta dauki mataki”.
Sun kara da cewa filayen da ake kokarin kwacewa su ne ginshikin rayuwarsu, la’akari da sune wuraren noman abincin su da kuma samun kudin shiga.
Mafari kenan da suka bukaci Gwamnatin Jihar Nasarawa da Hukumar Kula da Filaye da su dakatar da duk wani yunkuri na kwace filayen, har sai an gudanar da cikakken bincike tare da baiwa al’umma damar kare kansu.
Yayin da manema labarai suka isa Fadar Masarautar Keffi domin Jin ta bakin Mai Martaba Sarkin Keffi Dakta Cindo Yamusa, ya aiko Sakataren wucin gadi na Masarautar Malam Yakubu, ya sanar da ‘yan jaridun cewa, yana kan hanyarsa ta zuwa ta’aziyya a garin Nasarawa amma da zarar ya shirya zai kira su domin mayar da martani kan wannan zargi.











