Wani Dankshin kasa Abubakar Umar Oduwalle Adamawa ya bayyana Gwamna Abba Kabir Yusuf a matsayin shugaba Nagari da yake jinkan talakawa da bunkasa harkokin ilimi ta hanyar ciyar da dalibai yanmakarantar fimarairi da Basu kayayyakin makaranta da gyara hanyoyi da ba da tallafi da biyawa daliban Mayan makarantu Rabin kudaden karatu.
Abubakar Umar Oduwalle yace,Baya ga haka Gwamnan Kano ya dauki nauyin Yan jami’a zuwa Karo karatu kasashen wajen Wanda wannan ba karamin abun a Yaba bane da sauran aikace -aikace da ba za su lissafu ba.
Yace,babban abin daya yake yawo zuwa jihohi shine, Shekaru 37 da suka gabata iyayensa sun nemi yayi karatu,Amma saboda rashin ganewa da taurin Kai ya ki tsayawa yayi, Amma daga Baya ya ga abokanansa duk sun Zama manyan mutane Wanda daga nan ne ya yanke shawarar daya daina shaye shaye tare Fara wayar da Kan matasa Akan shaye shaye saboda Baya son abin daya afku akansa Kada ya Kara faruwa Akan wasu.
Oduwalle Adamawa ya bayyana cewar, ya taho tun daga jihar Adamawa ya wuce jihar Katsina domin yiwa iyalan murigayi tsohon Shugaban kasa Muhammad Buhari ta’aziyya bisa rasuwarsa.
Yace a lokacin da ya Shiga jihar Katsina domin ta’aziyya ya wuce garin kahuta Inda ya ga irin ayyukan da Rara kahuta yayi a cikin garinsa Wanda yayi titin da zai shigo garin kahuta da kuma,masallacin juma’a da makarantar islamiyya da sauran abubuwa da dama ciki har ba da tallafi ga alummar garinsa.











