Shugaban Majalisar Wakilai ta Tarayya, Abbas Tajudeen, ya kaddamar da wani kwamitin wucin gadi domin gudanar da bincike kan zargin cewa an kafa Kwamitin Shugaban Ƙasa na Bunƙasa Zuba Jarin Ƙasashen Waje (Presidential Foreign Investment Promotion Council – PFIPC) ba tare da ingantaccen tushe na doka ba.
Da yake jawabi yayin ƙaddamar da kwamitin a birnin Abuja ranar Litinin, Abbas Tajudeen ya bayyana cewa batun da aka bai wa kwamitin aikin bincike ya jawo hankalin jama’a sosai, kuma akwai buƙatar gudanar da cikakken bincike domin gano gaskiyar lamarin.
Ya ce ana sa ran kwamitin zai gudanar da aikinsa cikin adalci, gaskiya da bin doka, tare da gabatar da rahotonsa ga Majalisar Wakilai domin ɗaukar matakin da ya dace.









