Kungiyar kwadago ta Najeriya NLC ta buƙaci Gwamnonin da ba su iya biyan sabon mafi ƙarancin albashi na Naira 70,000 da su sauka daga mukamansu.
Hakan na zuwa ne a matsayin martani ga Gwamnan Jihar Gombe Inuwa Yahaya wanda a kwanakin baya ya bayyana cewa Gwamnatin sa ba za ta iya biyan sabon mafi ƙarancin albashin Ma’aikata na kasa ba.
Gwamna Yahaya wanda kuma shi ne Shugaban ƙungiyar Gwamnonin Arewa ya bayyana haka a lokacin wata ganawa da shugabannin kungiyoyin kwadago da kungiyoyin ‘yan kasuwa a gidan Gwamnati da ke Gombe.
A tsokacin da Gwamna Yahaya ya yi, Benson Upah Shugaban hulɗa da jama’a na NLC ya shawarci Gwamnan da ya yi murabus.
“Ya yi murabus idan ba zai iya biya ba, ya yi rantsuwar aiki don tabbatar da doka kuma ba zai karya ta ba,” in ji Upah.
Kun tuna cewa a makon da ya gabata ne Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya rattaba hannu kan sabuwar dokar mafi karancin albashi a hukumance ta maida mafi karancin albashin Ma’aikata zuwa Naira 70,000 daga Naira 30,000.
Wannan matsayar ta biyo bayan tattaunawar kusan makonni biyu da Shugaban ƙasar ya yi da kungiyoyin kwadago wadanda tun farko suka bukaci a biya su Naira 250,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi.
A ranar 18 ga watan Yuli ne Gwamnatin Tarayya, da kungiyoyin kwadago da masu zaman kansu suka kammala tattaunawa na tsawon watanni da suka kwashe suna tattaunawa kan mafi ƙarancin albashin Ma’aikata wanda hakan ya sa aka cimma matsaya kan adadin Naira 70,000 a kowane wata.
Daga bisani a ranar 15 ga watan Yuli Majalisar Zartaswa ta Tarayya ta dora wa Ministan Kasafin Kudi da Tsare-tsare nauyin shiryawa da gyara kudiri na gyara kasafin kudin 2024.
Mako guda kenan Shugaba Tinubu ya miƙa bukatar Majalisar dattawa ta gyara dokar kasafi ta 2024 da kuma dokar kudi ta 2023 inda ya bada shawarar a kara kasafin kudi da Naira Tiriliyan 6.
An aika wasikar ne zuwa ga Shugaban Majalisar Dattawa kuma aka karanta shi a yayin zaman Majalisar.












