Fitattun masana da yansiyasa irin su tsohon Mataimakin Shugaban kasa Atiku Abubakar, da Gwarzon kyautar Nobel, Farfesa Wole Soyinka, da Lauya mai kare hakkin ɗan Adam, Femi Falana (SAN) da wasu kungiyoyin farar hula (CSOs) sun caccaki Jawaban da Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi ga ƴan Najeriya inda suka ce bai yi magana kan muhimman batutuwan da suka shafi ƙasar ba waɗanda suka janyo zanga-zangar neman kawo ƙarshen Mulkin rashin adalci.
Masu Zanga-zangar da ta fara a ranar Alhamis kuma ta yi sanadin salwantar rayuka mutane da dama tare da lalata kadarori na Biliyoyin Nairori.
Hakan ya sa aka yi kira daga bangarori daban-daban ga Shugaba Tinubu da ya yi wa ƴan Najeriya jawabi domin kawar da damuwar da masu zanga-zangar da sauran ƴan ƙasar suka nuna ciki har da tsadar rayuwa da rashin tsaro a Kasar.
Shugaban ya yi kunnen uwar shegu inda daga bisani ya yi Jawabi a jiya Lahadi yana mai bayyana dalilan cire tallafin Man Fetur da kuma matsayar Naira, inda ya ce waɗannan na daga cikin sauye-sauyen da ya kamata a yi domin ci gaban Najeriya.
Tinubu ya kuma zayyana wasu daga cikin matakan da Gwamnatin sa ta ɗauka domin daƙile illolin waɗannan manufofin, yana mai cewa ‘yan Najeriya za su ci gajiyar hakan a nan gaba.
Sai dai jim kaɗan bayan jawabin, masu sharhi da sauran masu lura da al’amura sun ce jawabin Shugaban ba shi da wani amfani, yayin da masu zanga-zangar suka ce bai nuna wata alama da ke nuna cewa yana sane da ainafin matsalolin da kasar ke fuskanta ba,
Sun ce baya ga rashin yin magana mai Ma’ana kan batun dawo da tallafin Man Fetur da darajar Naira, jawabin nasa mai sakin layi 38 bai ce komai ba kan muhimmin batu wato – rashin tsaro – musamman a Arewacin Najeriya inda aka kori Miliyoyin manoma daga gonakinsu da gidaje.
Zanga-zangar da ake ci gaba da yi ta kara ɗaukar sabon salo a Arewa, inda masu zanga-zangar suka yi zanga-zanga a Kano, da Katsina, da Jigawa, da Sokoto, da Kebbi, da Zamfara, da Kaduna, da Yobe, da Borno, da Nasarawa, da Plateau, da Adamawa da kuma Babban Birnin Tarayya Abuja suna baje kolin alluna masu dauke da sakonnin da ke nuna bukatar magance yunwa da rashin tsaro. An kuma gudanar da zanga-zangar a yankin Kudu maso Yamma in ban da Jihar Ekiti; wato Kudu maso Kudu, amma mutanen Kudu maso Gabas ba su fito zañga-zañgãr ba.
Da yawa daga cikin waɗanda aka zanta da su a yayin zanga-zangar a wasu Jihohin Arewa kamar Katsina Zamfara da Sokoto sun ce duk da cewa su manoma ne, amma an mayar da su mabarata domin ba su da damar shiga gonakinsu a yanzu saboda ‘yan fashi da masu garkuwa da mutane sun addabi yankin.
A martanin da ya mayar kan matakin da Tinubu ya ɗauka kan zanga-zangar, Wale Soyinka a wata sanarwa da ya fitar a jiya ya bayyana damuwarsa kan yadda Shugaban ya yi watsi tare da bada damar harbi da kashe masu zanga-zangar da ke neman a samar da Shugabanci na gari.












