• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Yadda masana da manyan yansiyasa suka caccaki shugaba Tinubu

aksam by aksam
August 5, 2024
Reading Time: 2 mins read
0
Home LABARAI
ADVERTISEMENT
466
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Fitattun masana da yansiyasa irin su tsohon Mataimakin Shugaban kasa Atiku Abubakar, da Gwarzon kyautar Nobel, Farfesa Wole Soyinka, da Lauya mai kare hakkin ɗan Adam, Femi Falana (SAN) da wasu kungiyoyin farar hula (CSOs) sun caccaki Jawaban da Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi ga ƴan Najeriya inda suka ce bai yi magana kan muhimman batutuwan da suka shafi ƙasar ba waɗanda suka janyo zanga-zangar neman kawo ƙarshen Mulkin rashin adalci.

Masu Zanga-zangar da ta fara a ranar Alhamis kuma ta yi sanadin salwantar rayuka mutane da dama tare da lalata kadarori na Biliyoyin Nairori.

RelatedPosts

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa ƴar Tik-tok Dake Unguwar Ɗanbare A Jihar Kano

Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro

Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka

Hakan ya sa aka yi kira daga bangarori daban-daban ga Shugaba Tinubu da ya yi wa ƴan Najeriya jawabi domin kawar da damuwar da masu zanga-zangar da sauran ƴan ƙasar suka nuna ciki har da tsadar rayuwa da rashin tsaro a Kasar.

Shugaban ya yi kunnen uwar shegu inda daga bisani ya yi Jawabi a jiya Lahadi yana mai bayyana dalilan cire tallafin Man Fetur da kuma matsayar Naira, inda ya ce waɗannan na daga cikin sauye-sauyen da ya kamata a yi domin ci gaban Najeriya.

Tinubu ya kuma zayyana wasu daga cikin matakan da Gwamnatin sa ta ɗauka domin daƙile illolin waɗannan manufofin, yana mai cewa ‘yan Najeriya za su ci gajiyar hakan a nan gaba.

Sai dai jim kaɗan bayan jawabin, masu sharhi da sauran masu lura da al’amura sun ce jawabin Shugaban ba shi da wani amfani, yayin da masu zanga-zangar suka ce bai nuna wata alama da ke nuna cewa yana sane da ainafin matsalolin da kasar ke fuskanta ba,
Sun ce baya ga rashin yin magana mai Ma’ana kan batun dawo da tallafin Man Fetur da darajar Naira, jawabin nasa mai sakin layi 38 bai ce komai ba kan muhimmin batu wato – rashin tsaro – musamman a Arewacin Najeriya inda aka kori Miliyoyin manoma daga gonakinsu da gidaje.

Zanga-zangar da ake ci gaba da yi ta kara ɗaukar sabon salo a Arewa, inda masu zanga-zangar suka yi zanga-zanga a Kano, da Katsina, da Jigawa, da Sokoto, da Kebbi, da Zamfara, da Kaduna, da Yobe, da Borno, da Nasarawa, da Plateau, da Adamawa da kuma Babban Birnin Tarayya Abuja suna baje kolin alluna masu dauke da sakonnin da ke nuna bukatar magance yunwa da rashin tsaro. An kuma gudanar da zanga-zangar a yankin Kudu maso Yamma in ban da Jihar Ekiti; wato Kudu maso Kudu, amma mutanen Kudu maso Gabas ba su fito zañga-zañgãr ba.

Da yawa daga cikin waɗanda aka zanta da su a yayin zanga-zangar a wasu Jihohin Arewa kamar Katsina Zamfara da Sokoto sun ce duk da cewa su manoma ne, amma an mayar da su mabarata domin ba su da damar shiga gonakinsu a yanzu saboda ‘yan fashi da masu garkuwa da mutane sun addabi yankin.

A martanin da ya mayar kan matakin da Tinubu ya ɗauka kan zanga-zangar, Wale Soyinka a wata sanarwa da ya fitar a jiya ya bayyana damuwarsa kan yadda Shugaban ya yi watsi tare da bada damar harbi da kashe masu zanga-zangar da ke neman a samar da Shugabanci na gari.

Share186Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Mafi karancin albashi, NLC ta nemi gwamnan Gombe ya yi murabus

Next Post

Wani sanata ya fadi gaskiyar abin da yake damun Arewa da kuma yadda za’a iya gyara matsalar

aksam

aksam

RelatedPosts

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa  ƴar Tik-tok  Dake Unguwar  Ɗanbare A Jihar Kano
LABARAI

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa ƴar Tik-tok Dake Unguwar Ɗanbare A Jihar Kano

by aksam
June 20, 2026
Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro
LABARAI

Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro

by Khadija Maitaya
June 19, 2026
Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka
LABARAI

Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka

by Khadija Maitaya
June 16, 2026
China Ta Soke Darussa 12,000 na Jami’o’i Domin Shirin Zamani na AI
LABARAI

China Ta Soke Darussa 12,000 na Jami’o’i Domin Shirin Zamani na AI

by Khadija Maitaya
June 14, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Mafi karancin albashi, gwamnan Kano ya bi sahun na Legas da Rivers wajen fin gwamnatin tarayya albashi mai tsoka

October 29, 2024
Bayan kammala shan ruwa da jakadun kasashen Duniya Tinibu ya fadi abin da yafi damun sa a Najeriya

Bayan kammala shan ruwa da jakadun kasashen Duniya Tinibu ya fadi abin da yafi damun sa a Najeriya

April 8, 2024
ADVERTISEMENT

Trending.

Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

June 12, 2026
An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 1, 2026
The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

June 1, 2026
Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da  Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma  A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 5, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

June 15, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media