• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Wani sanata ya fadi gaskiyar abin da yake damun Arewa da kuma yadda za’a iya gyara matsalar

aksam by aksam
August 5, 2024
Reading Time: 3 mins read
0
Home LABARAI
ADVERTISEMENT
466
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Tsohon Sanata mai wakiltar Kaduna ta Arewa Sanata Shehu Sani ya ce lokaci ya yi da ’yan Arewa za su zargi kansu akan matsalolin da yankin ke fama da shi maimakon zargin wasu yankuna ko shuwagabanni.

Sani wanda ya rubuta a shafinsa na Facebook a ranar Lahadi ya koka da cewa yawancin makarantun Gwamnati a yankin kyauta ne amma har yanzu matasanmu ba sa son zuwa Makaranta.

RelatedPosts

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa ƴar Tik-tok Dake Unguwar Ɗanbare A Jihar Kano

Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro

Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka

Ya ce “Da yawa daga cikinmu ba sa son Matan su yi aiki ko kuma su yi amfani da basirarsu ko hikima don samun abin dogaro da kai ko kuma ba da gudummawar iyali, shiyasa idan muka mutu mukan bar su a matsayin zawarawa marasa abin yi cikin tausayi da neman ɗauki.

Yawancin Matasa ba sa son yin aiki a matsayin masu koyo ko yara a wuraren koyon sana’o’i ko wuraren sayar da kayayyaki saboda ba su da zuciya da haƙurin juriya wajen neman dukiya ta halal.

Iyaye da dama a yankunan karkara suna miƙa ’ya’yansu ga Malaman addini a cikin birane wanda kuma mafi yawa sukan dogara ne da yaran su yi bara ko sata don ciyar da kansa da baiwa iyayen sa. Bisa dalilai na kabilanci, mun kare, mun yaba kuma mun ƙi bin diddigin jagororin kasar nan da suka fito daga yankin a duk wata damar da aka bata tsawon shekaru hamsin.

‘Yan fashi da ’yan ta’adda da suke kashe jama’a da garkuwa da su, suna hana manoman mu noma a gonakinsu, suna hana ‘ya’yanmu zuwa Makaranta, ba daga wata ƙasa suke ba ko kuma daga yankin Kudu, sun fito daga gidajenmu da iyalanmu a Arewa.
Muna ibada da su a masallaci guda, Mun kasance tare a matsayin yanki ɗaya cikin aminci da ‘yan’uwantaka da soyayya, amma sai muka rabu muka fara kyamar kanmu ta bambancin fahimtar addini.

Ba ma zabar Mutanen da za su yi mana hidima; muna zabar Shugabanni ne waɗanda za su samar mana da Taliya da hatsi.

Mun shirya tare da yada duk wani makirci na addini don hana yaranmu rigakafin lafiya kyauta daga cututtuka wanda ka iya haifar da dubban daruruwan makafi, da guragu, da kurame da suka tashi a matsayin masu fama da cutar polio, ko glaucoma, ko kuturta suna barace-barace a garuruwan Arewa da kudu. Yawancin yaranmu Mata ba su da jarin kasuwanci na dubu 100, amma sun mallaki wayar iPhone wadda ta kai darajar Naira Miliyan 1.5, za ka samu
Ba su da jari na dubu 100 amma suna iya yin fafutuka don mallakar atamfar biki ta Naira dubu 50.

Mun hana yawancin ƴaƴanmu Mata damar wucewa Makarantar gaba da Sakandare saboda munanan hasashe game da manyan makarantun, Ba ma son yaranmu mata suyi aikin sanya Unifom, a duk lokacin da aka bude kofofin daukar ma’aikata a Hukumar Shige da Fice, da ta Rundunar ƴan Sanda, da Civil Defence ba za mu so su nema ba.

Lokacin da ‘ya’yanmu suka kammala karatu a jami’o’i Musamman jami’o’in Gwamnati galibin iyayen da suke zuwa bikin yaye ɗalibai da kuma yaba ƙwazon ‘ya’yansu iyaye ne daga yankunan Kudu, Yawancin kamfanonin mu na Kano, da Kaduna, da Jos an rufe su tun lokacin da ‘yan yankinmu ke kan mulki. Manoman mu na karkara har yanzu suna noma da fartanya a tsawon lokacin da ’yan yankin namu suka yi mulki. Noman Gyada da auduga duk sun ɓace tuntuni a yankunan namu.

Dukkanin kayayyakin gine-gine da shagunan sayar da magunguna da ke arewacin kasar, sana’o’i ne masu zaman kansu na mutanen da suka zo daga wasu yankuna, waɗanda ba wata Gwamnati bace ta tallafa musu da kasuwancin ba, A lokacin da ’yan yankinmu suka yi Mulki mun danganta talauci da rashin tsaro ga Allah da zunuban da muke aikatawa, amma yanzu sai mu danganta hakan da Shugabanni.

Abuja tana yankin Arewa ne, Shin akwai wanda zai iya bayyana dalilin da ya sa mutanen yankin suka kasa mamaye harkokin kasuwanci masu zaman kansu a Abuja, da Suleja, da Mararaba? To yanzu wa ya kamata a zarga da wannan?

“Allah ya bamu mafi girman ƙasa mafi yawan jama’a, mafi yawan yankuna da ke da albarkatu da dabbobi kuma ya bamu iko a tarihin mu.
Wanne daga cikin ni’imomin Ubangijinmu za mu iya musun cewa muna dashi a Arewa?
kashi 80 cikin 100 na matsalolinmu laifin mu ne da kanmu ba wani ba”.

Share186Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Yadda masana da manyan yansiyasa suka caccaki shugaba Tinubu

Next Post

IBB ya magantu kan rade-radin da ke cewa ya Na Son Sojoji Su Kwace Mulki

aksam

aksam

RelatedPosts

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa  ƴar Tik-tok  Dake Unguwar  Ɗanbare A Jihar Kano
LABARAI

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa ƴar Tik-tok Dake Unguwar Ɗanbare A Jihar Kano

by aksam
June 20, 2026
Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro
LABARAI

Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro

by Khadija Maitaya
June 19, 2026
Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka
LABARAI

Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka

by Khadija Maitaya
June 16, 2026
China Ta Soke Darussa 12,000 na Jami’o’i Domin Shirin Zamani na AI
LABARAI

China Ta Soke Darussa 12,000 na Jami’o’i Domin Shirin Zamani na AI

by Khadija Maitaya
June 14, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Muna Duba Yiwuwar Saka Dokar Ta Baci A Kan Barkewar Annobar Kwalara – Hukumar NCDC

Muna Duba Yiwuwar Saka Dokar Ta Baci A Kan Barkewar Annobar Kwalara – Hukumar NCDC

June 20, 2024
Ba Rabo Da Gwani ba Mayar Da Kamarsa Shekarau 50 Ke nan Da Kisan Murtala Ramat Muhammad

Ba Rabo Da Gwani ba Mayar Da Kamarsa Shekarau 50 Ke nan Da Kisan Murtala Ramat Muhammad

February 13, 2026
ADVERTISEMENT

Trending.

Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

June 12, 2026
An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 1, 2026
The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

June 1, 2026
Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da  Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma  A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 5, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

June 15, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media