• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Bayan kammala shan ruwa da jakadun kasashen Duniya Tinibu ya fadi abin da yafi damun sa a Najeriya

aksam by aksam
April 8, 2024
Reading Time: 1 min read
0
Home LABARAI
ADVERTISEMENT
467
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Shugaban tarayyar Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya kara isar da bukatar samun zaman lafiya a sassan da suke fama da yake-yake musamman a Afrika da sauran nahiyoyin duniya baki daya.

Mr. Bola Ahmed Tinubu ya bukaci hakan ne a fadarsa dake birnin Abuja yayin buda baki da jakadun kasashen duniya da shugabannin kungiyoyin kasa da kasa, ya ce akwai bukatar shugabannin kasashe su karkatar da hankulansu wajen tabbatar da zaman lafiyar duniya baki daya.

RelatedPosts

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa ƴar Tik-tok Dake Unguwar Ɗanbare A Jihar Kano

Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro

Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka

Shugaba Tinubu ya ce lokaci ya yi da ya kamata  shugabannin kasashe da kungiyoyin kasa da kasa na duniya su hada kan su tare da fito da wasu sahihan matakai na diplomasiyya da za su samar da mafita ta karshe wadda za ta dakile tasirin kungiyoyin ‘yan ta’adda da na masu tada kayar baya kana da rikice-rikien kabilanci da na addini.

Shugaban ya jaddada mahimmancin hakuri da juriya a matsayin manyan sinadaran samar da dauwamamen zaman lafiya da kwanciyar hankali a tsakanin al’ummar duniya, wanda hakan na daga cikin darasin watan azumin Ramadan.

“Na ji dadin kasancewar ku a nan, inda muke musayar bayanai a tsakanin mu, amma ya kamata a cikin zuciyarmu mu saka tausayi da jin kan marasa galihu wadanda ba su da wadata domin da su ne za mu hadu mu samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a duniya, ba za a taba samun wadatuwar tattalin arziki ba ba tare da zaman lafiya ba.”

Daga karshe shugaban na tarayyar Najeriya ya bukaci jakadun kasashen da su isar da sakonsa na zaman lafiya ga shugabannin kasashensu

Share187Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Sanatan APC ya caccaki Tinibu akan wasu dalilai masu muhimmanci

Next Post

Moon Sighting, Sultan gives order to look for crescent today Monday 8/4/2024

aksam

aksam

RelatedPosts

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa  ƴar Tik-tok  Dake Unguwar  Ɗanbare A Jihar Kano
LABARAI

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa ƴar Tik-tok Dake Unguwar Ɗanbare A Jihar Kano

by aksam
June 20, 2026
Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro
LABARAI

Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro

by Khadija Maitaya
June 19, 2026
Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka
LABARAI

Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka

by Khadija Maitaya
June 16, 2026
China Ta Soke Darussa 12,000 na Jami’o’i Domin Shirin Zamani na AI
LABARAI

China Ta Soke Darussa 12,000 na Jami’o’i Domin Shirin Zamani na AI

by Khadija Maitaya
June 14, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Shugaba Tinubu ya jagoranci sulhunta Wike da Gwamna Fubara da ya gaji shi

Shugaba Tinubu ya jagoranci sulhunta Wike da Gwamna Fubara da ya gaji shi

December 18, 2023
Ga Sakon Bangajiya Daga Bakin:-  Ango Ibrahim Ado Garba

Ga Sakon Bangajiya Daga Bakin:- Ango Ibrahim Ado Garba

April 22, 2024
ADVERTISEMENT

Trending.

Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

June 12, 2026
An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 1, 2026
The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

June 1, 2026
Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da  Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma  A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 5, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

June 15, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media