Sanata Mohammed Ali Ndume, ya koka kan ƙarin kuɗin wutar lantarki da aka yi a baya-bayan nan.
Ya soki lokacin yin ƙarin yana mai cewa ƴan Najeriya har yanzu suna cikin shan wahalar cire tallafin man fetur, cewar rahoton jaridar Daily Trust.
A wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar, Ndume ya yi Allah-wadai da matakin, ya kuma buƙaci gwamnatin tarayya da ta sake duba halin da ƴan Najeriya ke ciki.
Ndume ya kuma soki rashin tuntubar majalisar tarayya wajen ɗaukar wannan matakin.
A kalamansa: yace “Akwai kuskure a lokacin da aka yi ƙarin. Ƴan Najeriya na fuskantar ƙalubale masu yawa.
Ƙara ɗora musu wannan nauyin ba adalci ba ne. “Har yanzu ƴan Najeriya ba su gama farfaɗowa daga cire tallafin man fetur a shekarar da ta gabata ba.
Ƴan Najeriya da dama na ji a jikinsu kan hakan. Kuskure ne yanzu a zo da wannan ƙarin a wannan lokacin. “Hauhawar farashin kayayyaki ya yi sama sosai.
Farashin abinci, magunguna, sufuri da kuɗaɗen makaranta ya yi tashin gwauron zabi. Ba adalci ba ne a ƙara wani nauyi a wannan lokacin.











