Alummar Falanin Karamar Hukumar Garki dake a jihar jigawa sun bayyana halin ko in kula da Gwamnati ta yi da su,Musamman ta fannin Samar da Ruwan sha da Makaranta da kula da Harkokin Noma da Rashin ba su dama wajen yin Zabe.
Shugaban Alummar Fulanin Alh. Usman Wanda, Adamu Usman ya yi jawabi a madadinsa ya bukaci kungiyoyin da Uwa_Uba Gwamnati da ta yi bincike akan yadda Alummar ‘Yankukar Mikiya suke dannewa Sauran Alummar Hakkokinsu da kawo cikas wajen hanasu Zabar ra’ayinsu ta fannin Damokaradiyya.
Adamu Usman yace, yanzu haka Asibitin da za su rika zuwa domin duba lafiyarsu da ta iyalansu babu a Yankunan a don haka Kungiyar Fulanin take Neman Gwamnati da ta kawo musu daukin Gaggawa domin halin kunci Rayuwar da Rashin Kayayyakin more Rayuwa.
Ya bayyana cewa akwai bukatar Gwamnatn jihar jigawa da waiwayi wadan nan Alumma kasancewar su ma yanjihar ne kuma kungiyoyin su suna da rawar takawa wajen ci gaban Alummar Karamar Hukumar Garki,Musamman yakunan ‘Yankukar Mikiya.
A don haka yake kira ga Gwamnatin jihar jigawa da sauran masu Zuwa da tsaki,da su kawowa yankunan Fulanin Rugagensu domin samun damar aiwatar da kiwansu ta hanyar Samar musu gurin kiwo da Makarantu da hanya da wutar lantarki kamar Alummar dake Rayuwa a jihar jigawa, inda yace akwai kusan mutane Dubu daya da ‘Dari biyar da suke gudanar da rayuwa a yankin Wanda duk suna karkashin Karamar Hukumar Garki.
Adamu Usman ya kara da cewa,yakamata Gwamnatoci a matakai daban_daban su taimaka domin a rika basu damar yin zabe a duk lokutan da aka tashi yin Zabuka musamman, wannan lokacin da Zabukan Kananan Hukumomi yake Karatowa,saboda suna da kuri,’unsu domin Zabar Wanda suke ganin zai iya yi musu adalci dazarar ya dare Kujerar karagar Mulki.
COV/IBRAHIM SANI GAMA/












