DAGA HASSAN UMAR GWAMMAJA
Kotun koli ta yanke hukunci kan karar da gwamnatin tarayya ta shigar a kan gwamnonin jihohi 36 kan cin gashin kan kananan hukumomi.
Jaridar DAILY TRUST ta ruwaito cewa A cikin karar, Babban Lauyan Gwamatin Tarayya kuma Ministan Shari’a, Lateef Fagbemi (SAN), ya nemi cikakken ‘yancin cin gashin kai da kuma raba kudade kai tsaye ga kananan hukumomi 774 na kasar nan.
Ya bukaci kotun kolin da ta yi amfani da sashe na 1, 4, 5, 7 da 14 na kundin tsarin mulkin kasar domin bayyana cewa gwamnoni da majalisun jihohi suna da hakkin tabbatar da tsarin dimokuradiyya a mataki na uku.
A hukuncin da ta yanke wanda mai shari’a Emmanuel Agim ya karanta, kotun kolin ta bayyana cewa ba bisa ka’ida ba ne gwamnoni su rike kudaden da ake bukata na kananan hukumomi .












