Jigo kuma mai fafitukar rajin Dr.Nasuru Yusuf Gawuna yayi Nasara a kotun Daukaka Kara,Ya zama dawwamamme kuma,Halastaccen Gwamnan jihar kano, Alh.Usaini Gama,ya bayyana cewa, Nasuru Yusuf Gawuna shine Gwamnan jihar kano kamar yadda Kotu ta Sanar.
Alh Usaini Gama ya bayyana haka ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai dangane da yadda wasu Abokanan burmin siyasa suke ta sukan gwanin nasa wato,Dr.Nasuru Yusuf Gawuna.
Usaini Gama yace,Dr.Nasuru Yusuf Gawuna, Shine Wanda ya lashe zaben Gwamnan da aka yi,Sai dai wasu marasa kishin jihar kano, suka nemi yi masa magudi ta hanyar Aringizon kuri’u sama da dubu Dari da sitti,(16000)Sai dai ta ‘yan magana dake cewa:Biri yana ganinka mai ‘jar’ koma.
Wannan ce,ta sanya Usaini Gama ya ga dacewar ya mayar da martani ga masu kushe masa gwaninsa Saboda yadda wasu suke masa Hassada batare da ya mayar musu martani ba.
Usaini Gama yayi kira garesu da su zo su marawa Dr.Nasuru Yusuf Gawuna baya domin a ciyar da jihar kano da Alumma gaba,kasancewar ya rike mukamai da dama tun daga Shugaban Karamar Hukumar Nassarawa zuwa Kwamishina har ya zuwa Mataimakin Gwamna,Wanda ga shi yanzu ya zama tabbataccen Gwamnan jihar kano domin shi kotu ta tabbatar a matsayin Gwamna.
Yace, lokaci ya yi da yakamata ‘Yan’adawa su hakura da yin kiyayya da hassada da kushe ga mai rabo domin kuwa Dr.Nasuru Yusuf Gawuna yin Allah ne ba na mutum ba.
Haka Zalika Alh.Usaini Gama ya bukaci kungiyoyin Yankasuwa da na Dalibai da Alummar jihar kano da sauran ‘yanjamiyyar (APC)da su ci gaba da gudanar da add’u’oi yadda suka Saba a kodayaushe domin Insha Allahu Dr. Nasuru Yusuf Gawuna shine Gwamnan jihar kano koina ne.
A don haka yake kira ga masu fafutukar daukaka kara cewa,Mai gaskiya kar ya ji tsoron hassada balantana keta a cewar,Alh. Usaini Gama Dr.Nasuru Yusuf Gawuna shine Amsa ga kanawan Dabo.
Ibrahim sani gama pyramid radio.











