Hukumomin Chadi sun ce zaben shugaban kasar da aka jinkirta, a yanzu za a gudanar da shi a watan Mayu.
Ana sa ran zaben ya kawo karshen mulkin rikon kwarya da aka fara a 2021 lokacin da aka kashe tsohon shugaban kasar, Idriss Déby, a fagen daga, bayan shekara talatin (30) a kan mulki.
A wani mataki da ya saba wa tsarin mulki, an nada dansa Janar Mahamat Déby a matsayin magajinsa, inda ya yi alkawarin mayar da kasar ga mulkin dumukuradiyya.
An jinkirta zaben, kuma ana sa ran Janar Débyn ya tsaya takara.
Masu sharhi na cewa abu ne mai wuya a ce hukumar zaben kasar ta kasance ‘yar-ba-ruwanmu, kuma ‘yan hamayya na fargabar ci gaban mulkin iyalan gidan na Déby a Chadi.










