• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Kalli hanyoyin da zaka bi domin cin moriyar bashin karatu daga gwamnatin tarayya

aksam by aksam
July 19, 2024
Reading Time: 2 mins read
0
Home LABARAI
ADVERTISEMENT
466
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

A tsakiyar wannan mako ne shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya miƙa wa wasu Dalibai daga cikin waɗanda za su amfana da shirin bayar da rancen kudin karatu takardar samun bashing da suka nema, a ɗakin taro na fadar gwamnatin tarayya da ke Abuja.

Shirin, wanda ake kira NELFUND a turance, an fito da shi ne domin taimaka wa ɗalibai masu ƙaramin ƙarfi samun rancen kuɗi domin kammala karatunsu, inda za su biya bayan kammala makaranta, in ji shugaban asusun, Jim Ovia.

RelatedPosts

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano

Ya kuma bayyana cewa yawan mutanen da suka nemi karɓar bashin ya zuwa yanzu sun zarce 110,000 sannan kuma sama da mutum 160,000 ne suka ziyarci shafin neman karɓar bashin.

Bashin nawa za ku iya ci?

Yawan bashin da za a bai wa ɗalibi ya danganta ne da yawan kuɗin makaranta da kake biya, kasancewar bashin ba zai je ga aljihun ɗalibi ba.

Asusun bayar da bashin karatun zai biya makarantar da kake karatu isassun kuɗaɗe ne da za su isa a bar ɗalibi ya halarci darussa, rubuta jarrabawa da sauran abubuwan da suka shafi karatu.

Baya ga kudin makaranta, asusun bayar da bashin karatun zai kuma biya ɗalibi wasu ƴan kuɗaɗe da zai riƙe a hannu domin samun damar rayuwa a makaranta.

Asusun bai sanar da yawan kudin da zai bai wa ɗalibi a hannunsa ba, sai dai shugaban asusun ya ce kuɗaɗen a ƙayyade suke.

Yadda za ka nemi bashin karatu

Akwai matakai haɗu da ake bi wajen tura buƙatar neman bashin karatu na NELFUND.

Matakan su ne:

A ziyarci shafin Nelfund.

Yin rajista a shafin Nelfund ta hanyar shiga wurin da aka rubuta “APPLY NOW”.

A danna wurin tura buƙatar neman bashi “Request for Student Loan” domin cike fom.

A cike fom ɗin neman bashin sai a tura “Submit”.

A cikin fom ɗin da za a cike zai buƙaci mutum ya cika sunan makarantar da yake, da lambar karatu (matriculation number) da kuma ɗora takardun karatu.

Haka nan za ka bayyana matakin da kake na karatu.

Mun a nan tafe da yadda ake biya da kuma abubuwan da zasu Hana ka samu

Share186Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Dalilin da ya saka Sarkin Gaya ya sake zama sarki bayan tube su da aka yi a baya

Next Post

Yadda Yan Niger ke murna bayan da gwamnatin sojin kasar ta rage farashin man fetur da kaso mai tsoka

aksam

aksam

RelatedPosts

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan
LABARAI

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan

by aksam
May 4, 2026
Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano
LABARAI

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

by aksam
May 4, 2026
NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano
LABARAI

NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano

by Khadija Maitaya
May 4, 2026
Tsohon Dan Takarar Shugaban Kasa A  Jam’iyyar Labour Party, Peter Obi, Ya Sanar Da Ficewarsa Daga  Jam’iyyar Haɗaka Ya ADC
LABARAI

Tsohon Dan Takarar Shugaban Kasa A Jam’iyyar Labour Party, Peter Obi, Ya Sanar Da Ficewarsa Daga Jam’iyyar Haɗaka Ya ADC

by aksam
May 3, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Zamu ci gaba da baiwa Gwamnatin jihar Kano hadin Kai domin Samar da tsaro: shuagabancin kasuwar Rimi

Zamu ci gaba da baiwa Gwamnatin jihar Kano hadin Kai domin Samar da tsaro: shuagabancin kasuwar Rimi

August 20, 2025
Yadda Tattalin Arzikin Ƙasar China ya sami tagomashi da kaso 6.8% a Rabin shekara

Yadda Tattalin Arzikin Ƙasar China ya sami tagomashi da kaso 6.8% a Rabin shekara

July 15, 2025
ADVERTISEMENT

Trending.

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

May 4, 2026
Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr.  Usaini Sani Adamu !!!

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr. Usaini Sani Adamu !!!

April 24, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

April 20, 2026
Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

April 17, 2026
Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

April 8, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media