Iran Ta Gargadi Ƙasashen Tekun Fasha Kan Sabbin Hare-haren Amurka Duk Kasar Da Tabawa Amurka Dama Zata fuskanci Ramuwar Gayya Mai Zafi
Iran ta ce in har Amurka ta sake kai sabbin hare-hare a kan ƙasarta, cibiyoyin makamashi da sansanonin Amurka da ke faɗin yankin za su zama guraren hare-haren ramuwar gayya.
Ministan Harkokin Wajen Iran, Abbas Araghchi, ya buƙaci Saudiyya, Qatar, Turkiyya da sauran ƙawayen Amurka na yankin da su matsa wa Shugaban Amurka Donald Trump lamba domin ya kauce wa sabon farmakin soja, tare da komawa kan teburin tattaunawar diflomasiyya.
Iran ta ce a shirye take ta mayar da martani idan aka tilasta mata, amma ta jaddada cewa babban abin da ta fi bai wa muhimmanci shi ne warware rikicin ta hanyar tattaunawa da diflomasiyya.










