Gwamnatin Shugaba Tinubu ta sanar da bayar da umarnin ɓude iyakokin Nijeriya na kan tudu da ruwa domin shigo da wasu kayayyakin abinci ba tare da haraji ba na tsawon kwanakin 150.
Ministan Ayyukan Gona na Nijeriya Abubakar Kyari ya bayyana haka a wani taron manema labarai a ranar Litinin.
Daga cikin kayayyakin da aka amince a shiga da su ƙasar akwai alkama da shinkafa da masara da wake.
Kuna ganin hakan zai taimaka wajan sakko da kayan abinci ?












