Daga Hassan Umar Gwammaja
Rundunar Hisbah ta Kano ta kama wani kwamishinan Jigawa bisa zargin sa da lalata da matar aure.
Kwamishinan da hukumar ba ta bayyana sunansa ba, ya shiga hannu ne bayan ƙarar da mijinta ya shigar, inda yake zargin matar kuma uwar ’ya’yansa biyu na lalata da kwamishinan a bayan idonsa.
Wani jami’in hukumar ta Hisbah da ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyana wa Aminiya cewa sun kama kwamishinan da matar ne bayan jami’an Hisbar da mijin matar sun rutsa su a wani kango mallakin kwamishinan a cikin mota.
Ganin su ne kuma ya sanya matar ta yi yunƙurin guduwa a motar, inda ta buge mai gadin, kafin rundunar Hisbah ta samu nasarar tsayar da ita da nasu motocin.











