Gwamnatin Najeriya ta yi karin haske kan wata bukata da shugaban yan a ware, Sunday Igboho ya nema daga kasar Birtaniya
A ranar Lahadi ne shugaban yan a waren ya ce ya tura takarda ga firaministan Birtaniya kan neman ƙirƙiro kasar Yarabawa
Gwamnatin kasar Birtaniya ta tabbatar da cewa ta karbi takardar da Sunday Igboho ya rubuta amma ta fadi matsayin wasikar a wajen ta
Punch ta wallafa cewa martanin Birtaniya ya biyo bayan magana da ake ne a kan wata wasika da Sunday Igboho ya rubuta mata
Wasikar Sunday Igboho ga Birtaniya
A ranar Lahadi da ta wuce shugaban yan a ware na yankin Yarabawa, Sunday Igboho ya rubuta wasika ga kasar Birtaniya.
Sunday Igboho ya rubuta wasikar ne domin neman a marawa kudirinsa na samar da kasar Yarabawa baya wanda hakan ya jawo cece-ku-ce.
Birtaniya ta yi magana kan raba Najeriya
Kasar Birtaniya ta ce ta karbi wasikar Sunday Igboho da ya rubutawa Firaministan kasar a ranar Lahadi.











