• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Gaskiyar Yadda Aka Siyar da Gidan da Ake Rushewa a Rijiyar Lemo Ta Fito Fili

Khadija Maitaya by Khadija Maitaya
July 25, 2026
Reading Time: 2 mins read
0
Home LABARAI
ADVERTISEMENT
469
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Daga Abubakar Sadeeq

Bayan yaɗuwar hotuna da bidiyon wani katafaren gida da ake rushewa a Unguwar Rijiyar Lemo, tare da iƙirarin cewa an sayar da shi mako guda bayan rasuwar mai gidan, bincike ya gano cewa labarin ba haka yake ba.

RelatedPosts

Sarkin Zurmi Ya Rasu Bayan Shekaru Biyar A Kan Sarauta

Kano State Govt ends 50 year BUK/Rimin zakara Land Dispute

Yaki da harkar Daba a Jihar Kano

Gidan da ake magana a kai yana daga cikin tsofaffin kuma fitattun gidaje a Unguwar Rijiyar Lemo. Ana danganta shi da *Alhaji Muhammad (Sakwaya)* ne saboda shi ne ya gina gidan tun kimanin shekaru 30 da suka gabata, kusan a shekarar 1998, kuma ya shahara a unguwar. Sai dai *Alhaji Muhammad (Sakwaya) yana nan da ransa cikin ƙoshin lafiya, kuma ya riga ya rabu da gidan tun shekaru da dama da suka gabata*, don haka ba shi ne ya sayar da gidan a wannan karon ba.

Bayan hotuna da bidiyon rushewar gidan sun fara yawo a TikTok, WhatsApp, Facebook, X da sauran shafukan sada zumunta, wasu suka fara yaɗa cewa an sayar da gidan ne mako guda bayan rasuwar mai gidan, tare da iƙirarin cewa an sayar da shi kan kuɗi har biliyoyin naira.

Sai dai majiyoyi masu tushe sun tabbatar da cewa wannan ba gaskiya ba ne. A cewarsu, *mai gidan na baya* ya riga ya sayar da gidan tun watanni kafin rasuwarsa, an kuma kammala biyan kuɗin cinikin gaba ɗaya. Bayan haka, an ba shi sanarwar ya fice daga gidan, sai dai Allah Ya ƙaddara ya rasu kafin lokacin da zai bar gidan.

Majiyar ta kuma ƙaryata rahotannin da ke cewa an sayar da gidan kan *Naira biliyan 2*, *biliyan 1* ko *miliyan 200*, tana mai cewa waɗannan adadi jita-jita ne, ba tare da bayyana ainihin kuɗin cinikin ba.

Dangane da rushewar gidan kuwa, sabon mamallakin ya bayyana cewa tun farko ba niyyarsa ba ce ya ci gaba da amfani da ginin. Ya ce yana shirin rushe gidan ne domin gina shagunan kasuwanci, kasancewar filin na maƙotaka da *Kasuwar ‘Yan Hula ta ‘Yan Moji*, da ke Layin Makarantar Allo a Unguwar Rijiyar Lemo.

Binciken ya nuna cewa labarin da ake yaɗawa na cewa an sayar da gidan mako guda bayan rasuwar mai gidan ba daidai ba ne. Gaskiyar magana ita ce *an riga an kammala cinikin gidan tun kafin rasuwar wanda ke zaune a cikinsa, yayin da rushewar ginin kuma wani ɓangare ne na shirin sabon mamallakin filin.*

Share188Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Gwamnoni Shida Sun Yi Alƙawarin Farfaɗo da Masana’antar Yadi a Najeriya Bayan Ziyarar Yankin Masana’antu na Benin

Next Post

SITE VISIT – SHEIKH ABDULLAHI MAIKANO EDUCATIONAL COMPLEX 🇬🇭

Khadija Maitaya

Khadija Maitaya

RelatedPosts

Sarkin Zurmi Ya Rasu Bayan Shekaru Biyar A Kan Sarauta
LABARAI

Sarkin Zurmi Ya Rasu Bayan Shekaru Biyar A Kan Sarauta

by Khadija Maitaya
September 1, 2026
Kano State Govt ends 50 year BUK/Rimin zakara Land Dispute
LABARAI

Kano State Govt ends 50 year BUK/Rimin zakara Land Dispute

by Khadija Maitaya
August 31, 2026
Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro
LABARAI

Yaki da harkar Daba a Jihar Kano

by Khadija Maitaya
August 31, 2026
Babban Malami Ya Kalubalanci Gwamnoni da ’Yan Majalisa Bisa Rufe Cibiyoyi 10 Na Yin Fasfo
LABARAI

Babban Malami Ya Kalubalanci Gwamnoni da ’Yan Majalisa Bisa Rufe Cibiyoyi 10 Na Yin Fasfo

by Khadija Maitaya
August 30, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf;  Ya Bada  Goron Sallah Ga Mahajjatan Kano

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf; Ya Bada Goron Sallah Ga Mahajjatan Kano

May 14, 2024
Wani Mutum Ya Haƙo Gawar  ’Yar Uwar Sa Daga Kabari Ya Kai Banki…

Wani Mutum Ya Haƙo Gawar ’Yar Uwar Sa Daga Kabari Ya Kai Banki…

April 28, 2026
ADVERTISEMENT

Trending.

Masu Siye Da Siyar Da Filaye A  R/zakara Sunkoka Da Aibantasu Da Gwamnatin Kano Keyi.

Masu Siye Da Siyar Da Filaye A  R/zakara Sunkoka Da Aibantasu Da Gwamnatin Kano Keyi.

August 26, 2026
Cristiano Ronaldo Ya Auri Georgina Rodríguez

Cristiano Ronaldo Ya Auri Georgina Rodríguez

August 12, 2026
Wani Kauran Mata Ya Jikkata Wata Dattijuwa Bayan Ta Hana Shi Shiga Gurin Da Bai kamata Ba

Wani Kauran Mata Ya Jikkata Wata Dattijuwa Bayan Ta Hana Shi Shiga Gurin Da Bai kamata Ba

August 29, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Matar Aure Hukunci Bayan Samunta Da Watsa Tafasasshen Ruwa Ga Kishiyarta

Kotu Ta Yanke Wa Matar Aure Hukunci Bayan Samunta Da Watsa Tafasasshen Ruwa Ga Kishiyarta

August 7, 2026
Iran Ta Kakkabo Wasu Manyan Jiragen Yaƙi Na Amurka

Iran Ta Kakkabo Wasu Manyan Jiragen Yaƙi Na Amurka

August 14, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media