DAGA HASSAN UMAR GWAMMAJA
Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya kara kudin goron Sallah da ake baiwa mahajjatan jihar a lokacin Babbar sallah yayin da suke kasar Saudiyya don gudanar da aikin Hajji.
Babban Daraktan Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kano, Laminu Rabi’u Danbappa ne ya bayyana haka a wajen taron masu ruwa da tsaki na kaddamar da kwamitocin gudanar da aikin Hajji na bana 2024, wanda aka gudanar a Central Hotel a Kano ranar Litinin.
Danbappa ya ce gwamnan ya amince da karin kashi 100 na abun da Ake baiwa alhazan, daga Riyal 50 zuwa Riyal 100 ga daukacin maniyyata da jami’ai 3110.
“Yanzu mai girma gwamna ya ga ya dace a kara shi bisa la’akari da tsadar canji da kuma yadda aka rage kudin guzurin maniyata (BTA) na bana.
“Saboda haka ina amfani da wannan dama wajen gode wa gwamnan bisa wannan karamci da kuma yaba masa bisa irin goyon bayan da yake ba mu don ganin an samu nasarar gudanar da aikin Hajjin bana,” inji shi.
Shugaban riko na karamar hukumar Gezawa ya kuma bayar da gudunmawar Naira 100,000 ga dukkan maniyyatan karamar hukumar, yayin da na Tofa da Rimin-Gado suka bayar da kyautar SR100 ga kowane mahajjaci daga kananan hukumomin.










