Godwin Emefiele ya musanya zargin da ake yi masa na tafka barna a lokacin da yake rike da babban banki kasa na CBN.
Godwin Emefiele ya yi watsi da rahoton binciken da Jim Obazee ya yi a wani jawabi da ya fitar, Punch ta tabbatar da wannan labari.
Mista Godwin Emefiele ya saki jawabin ne a yammacin Lahadi, ya karyata zargin boye kudi a wasu bankuna da ke kasashen waje.
A Jawabin Emefiele ya zargi kwamitin Jim Obazeee da sharri saboda a bata masa suna a wajen mutanen Najeriya
“Ba Sabiu Tunde Yusuf Bane”, Emefiele Ya Bayyana Wanda Ya Bada Umurnin Sauya Fasalin Naira Mista Godwin Emefiele ya saki jawabin ne a yammacin Lahadi, ya karyata zargin boye kudi a wasu bankuna da ke kasashen waje.
A jawabin da ya yi, Emefiele ya ce rahoton ba komai ba ne sai yunkurin bata sunan shi, ci masa mutunci saboda son ran mai binciken.
Ganin halin da yake ciki, tsohon gwamnan ya ce an ba shi shawarar ya yi shiru, lauyoyinsa za su dauki matakin da ya dace a kotu.
Duk da haka, Emefiele ya ce dole ya yi magana a game da wasu zargin da aka jefe shi da su, wanda ya ce sam ba su da alaka da gaskiya.
Rahoton ya yi ikirarin an cire $6.23m daga asusun CBN a kan umarnin bogi da sa hannun Muhammadu Buhari GCFR da Boss Mustapha.










