Daga: Hassan Umar Gwammaja
Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya bayyana hakan ne a zantawarsa da DCL Hausa a wani faifan bidiyo kan jita-jitar alkawarin takara da ake yi kan tsohon Dan takarar Gwamnan Kano Dr. Nasir Yusuf Gawuna, da kuma makomar tsohon mataimakin Gwamnan Kano Comrade Aminu Abdussalam Gwarzo Murabus.
In da Kwankwaso ya ce zuwa yanzu babu wanda aka yi wa al’kawarin wata takara. Sai dai ya ce ba za su bar wadanda suka wahalta musu haka kawai ba, face am basu mukamai a gwamnatin jiha da kuma ta tarayya idan sun yi nasara a zaben 2027











