Daga: Hassan Umar Gwammaja
Cikin Girmamawa Da Kyakkyawan fata Ƙungiyar Ihsan Development Forum tana tunatar da Hukumar Tsarawa Da Fidda Tasawirar Filaye Ta Jihar Kaduna “KADGIS ” Data cika Alkawarin data Dauka na Samar da dai-daito a tsakanin Al’ummar Garin Mahuta Dake Karamar Hukumar Igabi, Kaduna masu Gonaki da Gwamnatin Jihar da Kuma wasu dai-dai Kun Jama’a, Saboda tun Ranar da Hukumar ta “KADGIS” Karkashin Jagorancin Dakta Bashir Garba Ibrahim ta Aiko Mana Da Takardan GAYYATAR a Ranar 23 ga Watan Yunin Wannan Shekara, ta 2025, da cewa Ana Neman mu a Ranar 25 ga Watan Yunin Wannan Shekara ta 2025.
Wanda Kuma muka Amsa GAYYATAR zuwa Ofishin Hukumar Dake Kantitin Ali Akilu Unguwar Sarki Kaduna.
Don Haka Idan Mai Girma DG. Zai iya tunawa a ranar da muka zauna Bayan dukkannin bayanai sun gabata, ya yi Mana Alkawarin Baiwa kowa hakkin sa,
Wanda Kuma duk muka kyautata mashi zaton Hakan, To sai dai Tunda Daga wancan lokaci Babu wata Magana Mai karfi Sai ma ta kokarin yanke sadarwa a tsakani, in Banda lokacin da suke Neman dasa harsashin ginin wani Masallachi a wani Sashi na Daga cikin Filayen namu to ayayin da Manoma Suka Hana, shi ne Suka nemi Kungiya tare da Rokon a yi Hakuri a Bari a cigaba da gudanar da wancan Aiki na ginin Masallachi Nan ma Tare Da yin Alkawarin warware matsalar akan lokaci Domin Kawo karshen takaddamar Dake tsakani.
To Shi ma dai har ya zuwa wannan lokaci ji kake shiru, To bamu Sani ba ko yanayin Ayyukan ne ? ko Kuma sun Manta ne ? ba mu sani ba, shi yasa mu kace to bari mu yi TINI saboda Al,umma suna ta tambaya Domin Jin Ina Aka kwana ?
Saboda Haka Muna Kara yin TINI tare yin Kira ga dukkannin Wadanda Abun ya shafa da su Yi kokarin Kawo karshen wannan matsala Domin cigaba da Samun zaman lafiya Mai Dorewa a Jihar Kaduna Wanda shi ne Babban Burin Mai Girma Gwamna Sanata Dakta UBA SANI CON,
Mun gode.











