Daya daga cikin iyalan marigayi Alhaji Aminu Alhassan Dantata ya bayyana cewa marigayin ya bar umarni tun kafin rasuwarsa cewa a binne shi a birnin Madina, kusa da kabarin matarsa, marigayiya Hajiya Rabi Tajo Dantata.
Hajiya Amina Umar Fulani, wacce ita ce ‘yar uwa ga uwar gidan marigayin, ta shaida hakan a hirarta da wakilin Kadaura24 na TST Hausa a safiyar Asabar.
An Gurfanar da Matashi Bisa Zargin Yunkurin Kashe Kansa A Kan Allon Talla A Kano
A cewar Hajiya Amina, marigayi Aminu Dantata ya bayyana wannan bukata tasa tun bayan rasuwar matarsa a birnin Madina shekaru biyu da suka gabata.
“Ya yi wasiyya tun bayan rasuwar matarsa cewa idan shi ma Allah Ya karbi rayuwarsa, a binne shi a Madina kusa da ita,”
Tun da safiyar Asabar, shugaban majalisar malamai ta jihar Kano, Sheikh Ibrahim Khalil, ya sanar da cewa za a gudanar da sallar Ga’ib ga marigayi Alhaji Aminu Dantata a masallacin Juma’a na Aliyu Bin Abi Dalib da ke Dangi a Kano, da misalin karfe 2:00 na rana.
Rahotanni sun bayyana cewa marigayin ya rasu a birnin Dubai, kuma daga can ne za a dauki gawarsa zuwa Madina domin cika burinsa na yin hutun karshe a birnin Annabi Muhammad (SAW).
Marigayi Alhaji Aminu Dantata ya rasu yana da shekaru 94, bayan barin tarihi mai dimbin daraja a fannin kasuwanci, sadaka da kuma alheri ga al’umma baki daya.











