Dakarun Sojojin Najeriya na Operation Hadarin Daji sun kama wasu mutane uku da ake zargin suna safarar muggan makamai zuwa jihar Zamfara
Mutanen da aka kama a kan iyakar Illela da ke jihar Zamfara sun hada da wani da aka ce shugaban jam’iyya ne a gundumar Birnin Yero da ke Karamar Hukumar Shinkafi
Rahotanni sun nuna cewa jami’an tsaron sun samu ingantattun bayannan sirri ne dangane da wadanda ake zargin kuma suka kafa shingen bincike suka cafke su a hanya
Daga cikin wadanda ake zargin, akwai wani da aka ce shugaban jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) ne a gundumar Birnin Yero da ke Karamar Hukumar Shinkafi na jihar Zamfara.
Majiyar ta kara da cewa: “Dakarun hadin gwiwa na Operation Hadarin Daji na shiyyar Arewa maso Yamma sun samu ingantattun bayanan sirri game da ayyukan wani hatsabibin mai dillancin bindigu da ke nufin fasakwabrin makamai zuwa Zamfara, nan take sojojin suka kafa shingen hanya kuma suka kama mutum 3 da ake zargi.
“Mutane ukun da ake zargi suna Musa Usman Suen, Aminu Ibrahim, da Isah Mohammed da aka kama a baya-bayan nan a Shinkafi a ranar 22 ga watan Janairun 2024, an kwace tsabar kudi naira miliyan biyu da dari biyar da dubu tamanin, mota kirar Volkswagen Wagon, wayoyin salula 3 da wasu kayan daga hannunsu.”










