DAGA HASSAN UMAR GWAMMAJA
Yan bindiga sun saki ɗaliban makarantar Kuriga 287 da suka sace a Jihar Kaduna.
Ɗaliban sun shaƙi iskar ’yanci ne bayan shafe kimanin kwanaki 16 a hannun ’yan bindigar da suka yi garkuwa da su.
Gwamna Uba Sani ne ya sanar da hakan cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook da tsakar dare wayewar gari yau Lahadi.
Gwamnan dai bai yi wani ƙarin bayani kan yadda aka saki ɗaliban ba, ya dai gode wa Shugaban Kasa Bola Tinubu bisa tabbatar da ganin an sako ɗaliban ba tare da an “cutar da su ba.”









