Daga Khadija Muhammad Maitaya.
Tsohon Mataimakin Shugaban Najeriya kuma ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar ADC, Atiku Abubakar, ya sake jaddada cewa idan ya samu nasara a zaɓen shekarar 2027, zai dawo da tallafin man fetur.
Atiku ya bayyana hakan ne yayin da yake karɓar shugabannin jam’iyyar ADC na jihar Osun a Abuja, inda ya ce matsayinsa kan batun tallafin man fetur bai sauya ba.
Ya kuma yi watsi da wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Paul Ibe, ya yi, wadda ta nuna cewa za a dawo da tallafin ne na ɗan lokaci kafin daga bisani a cire shi.
Atiku ya ce Paul Ibe bai yi magana ne a madadinsa ba, yana mai cewa Najeriya ƙasa ce mai arzikin da za ta iya kula da jin daɗin al’ummarta.
Ya ce cire tallafin man fetur ya ƙara jefa ’yan Najeriya cikin tsananin wahalar rayuwa, don haka gwamnatinsa za ta mayar da hankali wajen rage tsadar samarwa da sufuri, da kuma ƙarfafa matatun man fetur na cikin gida.
Atiku ya ce babban burinsa shi ne rage tsadar rayuwa da kuma ƙara darajar kuɗin Najeriya a aljihun ’yan ƙasa.










