Daga Abubakar Suleiman
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasa Ajuri Ngelale ya sanyawa hannu kuma aka rabawa manema labarai.
Sai dai sanarwar ta ba bayyana takamaiman ranar da shugaban kasa zai dawo Nigeria ba.
” Shugaba Tinubu zai dawo Nigeria bayan ya kammala ‘yar gajeriyar ziyarar aiki da ya kai kasar ta faransa.
Idan za a iya tunawa Aksam Media ta rawaito a makon da ya ke karewa Shugaba Tinubu ya ziyarci kasar Equatorial Genie domin sanya hannu kan wata yarjejeniya.











