Daga Hassan Umar Gwammajaa
Sakamakon mummunan kamfar ruwan da ake yi a gonaki da kuma karancin abinci a jihar.
Kwamishinan aikin gona Mr Timothy Ojomah da shugaban kungiyar manoma, AFAN, na jihar, Salihu Adobayi, su ne suka yi kiran a wata tattaunawa da kamfanin dillancin labaran Najeriya, NAN, a Lokoja.
Suka ce tsawon sama da wata daya yanzu babu ruwan sama, kuma illar rashinsa za ta shafi tallafin da gwamnati ta bai wa manoma don bunkasa samar da abinci a jihar.
Shugaban kungiyar manoman ya ce kafin a shiga wannan yanayin na rashin ruwan, yanayin damunar ya karfafa wa manoma gwiwa a jihar.
”Abin takaici yanzu abin da muke fuskanta a fadin jihar shi ne rashin ruwa. Rashin ya shafi dukkanin abubuwan da aka shuka, musamman ma shinkafa fa masara..” in ji shugaban.











