Gwamnatin Jihar Kano tace ta karɓi korafe-korafen Ƙungiyoyi da ɗai-ɗaikun Jama’a akan ta binciki zargin almundahanar kudaden Ƙananan Hukumomin jihar, da’akeyiwa Me ɗakin tsohon Gwamna Dr. Abdullahi Umar Ganduje.
Kwamishinan Ƴada Labarai na Jihar Kano Baba Halilu Ɗantiye ne dai ya bayyana hakan inda yace nan gaba kaɗan Gwamnati zata duba yiyuwar hakan domin tabbatar da cewa anyiwa ko wanne bangare adalci.









