Majalisar wakilai sun bukaci Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya dakatar da yarjejeniyar SAMOA wanda take da alaka da daidaita yanci ga kowanne jinsi a nahiyar Afirka.
Rukunin Yan majalisa 88 ne ciki har da Dan majalisa mai wakiltar Karamar Hukumar Dala Aliyu Sani Madaki suka shigar da motion na neman Tinubu ya dakatar da yarjejeniyar
Majalisar ta nada kwamitin da zai jagoranci gudanar da bincike domin Gano abubuwan da yarjejeniyar ta kunsa












