• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Yadda NCDC ta dukufa domin gano cutar da ke yadu wa a jihar Arewa

aksam by aksam
April 18, 2024
Reading Time: 2 mins read
0
Home LABARAI
ADVERTISEMENT
471
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Yayin da cibiyar da ke yaki da yaduwar cututtuka ta Najeriya ke gudanar da bincike a kan wata cuta da ta bulla a Sakkwato, wadda ba a gane kanta ba, yanzu haka cutar na ci gaba da yaduwa .

A wannan ranar ta Alhamis ce dai ake sa ran babban daraktan cibiyar zai ziyarci Sakkwato don kara matsa kaimi ga binciken gano cutar da abin da ke kawo kamuwa da ita.

RelatedPosts

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano

Tun a watan Maris da ya gabata ne aka samu bullar cutar, wadda ke kawo kumburin ciki da ciwon zuciya, a wasu yankuna na karamar hukumar mulkin Isa da ke gabashin Sakkwato, sai dai jami’an lafiya na yankin ba su kai rahoton bullar cutar ba, sai da aka kawo wasu da suka kamu da cutar a asibitin koyarwa ta jami’ar Usmanu Danfodiyo dake cikin birnin Sakkwato.

Kwamishinan lafiya ta jihar Sakkwato Asabe Balarabe ta nuna bacin rai a kan rashin sanar da bullar cutar har ta kama mutane talatin da biyu, inda daga baya gwamnati ta sanar da hedikwatar cibiyar hana yaduwar cututtuka ta Najeriya don daukar matakin da ya kamata.

Cibiyar dai nan take ta aika da jami’anta domin gudanar da bincike, inda suka dauki samfurin abubuwa a yankunan da cutar ta bulla don bincike, sai dai kawo yanzu ba a kai ga gano abin da kawo cutar ba, acewar Dokta Nuhu Aliyu Dogon Daji, jami’i mai kula da yaduwar cututuka da annoba a jihar Sakkwato.

To sai dai duk da haka, jagoran ayarin kwararri masu kawo dauki na cibiyar hana yaduwar cututuka ta Najeriya Mr. Tajudeen Orowola, lokacin da yake yi wa mataimakin gwamnan jihar Sakkwato, Muhammad Idris bayani a kan cutar yace tuni sun tura dukan sanfurin da suka dauka a cibiyoyin gudanar da bincike a sassa daban daban kuma suna kan aikin binciken cutar.

A cewar sa da zaran sun kammala bincike suka bayar da rahoto za a san abinda kan kawo kamuwa da wannan cutar da kuma yadda za a shawo kan kamuwa da ita.

Zuwa yanzu dai cutar da ta bulla a karamar hukumar Isa, ta yadu zuwa makwabtan kananan hukumomi, a cewar jami’in kula da yaduwar cututuka da annoba, Dokta Nuhu Aliyu.

Dokta Nuhu Aliyu ya ce yau ne a ke sa ran babban daraktan cibiyar hana yaduwar cututuka ta kasa zai zo a Sakwwato domin karfafa guiwar aikin gano cutar da daukar matakan shawo kanta.

Sai dai wata matsala da masana suka ce tana addabar Najeriya kan gudanar da binciken cututuka ita ce rashin isassun wuraren bincike da ke da dukkan kayan aikin da ake bukata ga gudanar da bincike, abinda suke ganin akwai bukatar kara mayar da himma domin shawo kan wannan matsalar.

Share188Tweet118SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Yadda hatsari ya hada da wasu motoci dauke da fasinjoji

Next Post

Yadda aka dakile wasu Hare-haren Isra’ila a Iran da Iraq da kuma Syria

aksam

aksam

RelatedPosts

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan
LABARAI

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan

by aksam
May 4, 2026
Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano
LABARAI

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

by aksam
May 4, 2026
NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano
LABARAI

NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano

by Khadija Maitaya
May 4, 2026
Tsohon Dan Takarar Shugaban Kasa A  Jam’iyyar Labour Party, Peter Obi, Ya Sanar Da Ficewarsa Daga  Jam’iyyar Haɗaka Ya ADC
LABARAI

Tsohon Dan Takarar Shugaban Kasa A Jam’iyyar Labour Party, Peter Obi, Ya Sanar Da Ficewarsa Daga Jam’iyyar Haɗaka Ya ADC

by aksam
May 3, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Wani Gwamna ya amince da 80,000 ga maaikatan kananan hukumomi

Wani Gwamna ya amince da 80,000 ga maaikatan kananan hukumomi

December 11, 2024
NLC zata bukaci miliyan daya mafi karancin Albashi: Joe Ajaero

NLC zata bukaci miliyan daya mafi karancin Albashi: Joe Ajaero

February 12, 2024
ADVERTISEMENT

Trending.

Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr.  Usaini Sani Adamu !!!

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr. Usaini Sani Adamu !!!

April 24, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

April 20, 2026
Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

May 4, 2026
Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

April 17, 2026
Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

April 8, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media