Rahotanni da ke shigowa yanzu haka sun nuna cewa an harbe wakilin jam’iyya har lahira a garin Ogoja da ke yankin arewacin jihar Kuros Riba.
Jaridar Daily Trust ta rahoto cewa an harbe mutumin ne a wani wuri kusa da Rumfar zaɓen da ke yankin. Jami’ar hulɗa da jama’a ta rundunar ‘yan sanda reshen jihar Kuros Riba, Irene Ugbo, ta tabbatar da faruwar lamarin lokacin da ta halarci wani shirin gidan Radiyo. Mai magana da yawun rundunar yan sandan ta ƙara da cewa kamata ya yi jami’an hukumar soji su tsaya nesa da wurin kaɗa kuri’a.
Menene asalin abinda ya faru?
Wani ganau da abun ya faru a gabansa ya ce mamacin, wanda ake kira da suna, Joe a taƙaice, sanannen ɗan Acaɓa ne a Kalaba, babban birnin jihar Kuros Riba.
Kawo yanzun da yawan masu kaɗa kuri’a da suka fito zabe sun tsaya cirko-cirko sakamakon kisan wakilin jam’iyyar a kusa da rumfar zaɓensu.











