Gwamnan babban bankin Najeriya CBN, Olayemi Cardoso, ya nesanta kansa daga zama sababin halin kuncin da ‘yan Najeriya ke ciki a halin yanzu.
Jaridar Daily Trust ta rahoto cewa ‘yan Najeriya sun koka kan halin matsin tattalin arzikin da kasar ke ciki sakamakin tsare-tsaren da gwamnati ta ɓullo da su da sunan garambawul.
Tun a watan Mayu, 2023 a wurin bikin rantsar da shi, shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kudurinsa na yin sauye-sauye, inda nan take ya tabbatar da tuge tallafin man fetur.
Bayan haka kuma shugaban ƙasar ya kuma ɗauki matakin zare hannun gwamnati a hada-hadar kudin Najeriya watau Naira, PM News ta rahoto.
CBN ne ya jawo halin matsin da ake ciki a Najeriya?
Da yake jawabi ranar Talata a taron farko na kwamitin kula da harkokin kudi (MPC) karkashin jagorancinsa, Cardoso ya ce ba shi da hannu a jefa kasar cikin ƙaƙanikayi.
Gwamnan babban bankin Najeriya, Cardoso ya ce shi da tawagarsa ba su da hannu a matsalolin tattalin arzikin da ‘yan Najeriya ke fuskanta.
Ya ba da tabbacin cewa babban bankin na daukar matakan da suka dace don ganin an dawo da harkokin kudi kan turba, kamar yadda yake a baya.
Da yake amsa tambaya kan ko manufofin da CBN ya bullo da shi a karkashinsa ne ya jefa ƙasar nan cikin wannan hali, Cardoso ya ce:











