Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinibu ya nada surukinsa a matsayin wanda zai jagoranci hukumar samar da gidaje ta kasa, FHA, wani al’amarin da ya janyo cece-kuce tsakanin ‘yan Najeriya, inda suke alakanta abin da nuna son kai
Wannan ne dai karon farko da shugaba Tinubun ke nada wani daga cikin iyalinsa a wani matsayin jagoranci a matakin gwamnatin tarayya.
Fadar shugaban kasa ta sanar da cewa “Mista Ojo na da ” gogewa na fiye da shekaru 10 a harkar gidaje da otal-otal. Sannan kuma tsohon dan majalisar tarayya ne.”
To sai dai ‘yan Najeriya na ci gaba da mayar da martani dangane da nadin, inda wasu ke cewa akwai mutanen da suka fi shi goge da cancanta.
Nada mista Ojo dai a cewar mai magana da fadar shugaban kasa shi ne ” kokarin yi wa hukumar samar da gidaje ta gwamnatin tarayya garambawul.












