Wata Kotun shari’ar Musulunci a nan jihar Kano, ta aike wani mutum mai suna Murtala Adamu, gidan gyara hali da tarbiya na tsawon watanni shida saboda laifin aikata badala.
Kamar yadda jaridar Aminiya ta ruwaito, an kama Adamu ne tare da shahararriyar ‘yar TikTok, Murjanatu Ibrahim Kunya, wacce aka fi sani da Murja Kunya.
Kotun wacce ke zamanta a unguwar Gama, karamar hukumar Kumbotso, ta kuma bai wa matashin zabin biyan tara ta N30,000 kan samunsa da laifin tayar da zaune tsaye da aikata aikin assha.
Mai gabatar da kara, Aliyu zainul Abidin, ya sanar da kotun cewa an kama Murtala ne tare da Murja a unguwar Hotoro.
Ya kuma ce an yi kamun ne bayan samamen da dakarun hukumar Hisbah suka kai bayan korafe-korafen da suka samu daga mazauna yankin.
Kotu ta hana matashin shiga unguwar Hotoro na tsawon shekaru 2 Har ila yau, Zainul Abidin ya bayyana cewa laifukan da ake tuhumar Murtala Adamu da aikatawa sun yi karo da sashi na 275 na kundin dokokin final-kot.
Kan haka ne, Mai Shari’a Malam Nura Yusuf Ahmed, ya yanke masa hukuncin daurin watanni shida ko zabin biyan tara ta Naira 30,000











