Wasu ƴan bindiga da ba a sani ba sun halaka Barista Victor Onwubiko, a kan hanyarsa ta komawa jami’ar jihar Abia daga mahaifarsa da ke Imo
Rahotanni sun bayyana cewa lauyan ya rasa ransa ne ranar Asabar da daddare a kan titin Okigwe zuwa Oturu, wanda ake yawan kai hare-hare
Mai magana da yawun ƴan sandan jihar Imo, Henry Okoye, ya tabbatar da faruwar lamarin ranar Litinin, 12 ga watan Fabrairu
Wata majiya ta bayyana cewa lamarin ya faru ne a kan hanyar Okigwe/Uturu tsakanin karfe 8 zuwa 9 na dare a ranar Asabar 10 ga watan Fabrairu, 2024.
A cewar majiyar, ƴanbindigar sun yi ajalin fitaccen lauyan ne yayin da suka kai farmakin satar mutane a kan titin da daddare.
“Ƴan bindiga sun kashe lauyan wanda daga bisani aka gano sunansa, Barista Victor Onwubiko a kan titin Okigwe. Mamacin ɗan asalin garin Okigwe a jihar Imo ne amma yana rayuwa a jami’ar jihar Abia da ke Uturu.”
“Yana kan hanyar komawa jihar Abia inda yake zaune kwatsam sai ‘yan bindiga suka yi masa kwanton bauna, suka kashe shi a titin Okigwe/Uturu.”
“A ƴan kwanakin nan ana ta fama da hare-haren satar mutane a wannan titin duk da tulin jami’an tsaron da ke jibge a wurare daban-daban na titin.”












