Babban lauya kuma ɗaya daga cikin waɗanda suka shirya zanga-zangar yunwa a Najeriya, Ebun-Olu Adegboruwa, SAN, ya fitar da wuraren da za a gudanar da zanga-zangar a faɗin Najeriya
Adegboruwa, a wani martani da ya yiwa IGP Kayode Egbetokun, ya lissafo muhimman wurare a jihohi tara daga cikin 36 na ƙasar nan, ciki har da babban birnin tarayya Abuja
Jerin wuraren zai ƙara faɗaɗa kuma wasu jihohi za su iya shiga kamar yadda lauyan ya buƙaci IGP Kayode Egbetokun ya ba su ƴan sandan da za su ba su kariya
A yayin taron, Kayode Egbetokun ya buƙaci a gudanar da zanga-zangar a keɓaɓɓun wurare yayin da masu shirya ta suka haƙiƙance sai sun fito kan tituna, cewar rahoton tashar Channels tv.
Jaridar Leadership ta ruwaito cewa, bayan babban sufeton ƴan sanda,
Kayode Egbetokun ya buƙaci a bayyana wuraren,
Adegboruwa ya samar da wuraren kamar haka:
Eagles Square, Abuja Alausa Park,
jihar Legas Gidan mai na Rosewale,
hanyar Iwo, Ibadan, jihar Oyo Freedom Park, Oshogbo,
jihar Osun Kusa da makarantar noma,
jihar Bauchi Kusa da bankin Wema,
Akpakpava Lane, birnin Benin, jihar Edo
Shataletalen Maiduguri, jihar Borno
Kusa da filin ƙwallo na jihar Yobe da ke Damaturu, jihar Yobe
Shataletalen Rainbow da filin ƙwallo na Pantani, jihar Rivers












