An yabawa Gidauniyar ba da tallafi da taimako ta Lafiya Sak dangane da tallafi da taimako da take baiwa Alumma a fadin jihar Kano,Musamman a fannin kiwan lafiya.
Shugaban Kungiyar Matasan Unguwar Dorayi yamadawa kuma, Dankishin kasa Aminu Abdullahi Bello Bayero ne ya yi yabon a lokacin da yake zantawa da manema labarai a yankin Karamar Hukumar Gwale.
Aminu Abdullahi Bayero yace,a matsayinsu na Kungiyar Matasan Unguwar Dorayi suna yawan ziyartar Asibitocin dake jihar nan domin ba da tasu Gudunmawar Wanda a nan ne suka ji Alumma da marasa lafiya na yabon Shugaban Gidauniyar Dr.Zaharadden Adam Zakirai akan yawan tallafin da yake bayarwa a Asibitoci.
Aminu Abdullahi Bayero, yace hakan ta sanya suka ga dacewar su yabawa wannan Bawan Allah domin kara masa kaimi da karsashi da kuma,sanyawa sauran yanuwa da masu hannu da Shuni Sha’awar aiwatar da irin wannan ayyukan Alkairi ga masu bukatar taimako.
Shugaban ya bayyana cewa, Akwai bukatar Gwamnati da masu hannu da shuni su rika baiwa irin wadannan Gidauniya tambobin yabo domin kara musu kwarin gwiwa akan ayyukan tallafi da taimako da suke gudanarwa daga lokaci zuwa lokaci.
Yace, Dr. Zaharaddeen Wanda shine Shugaban Gidauniyar Lafiya Sak,yana ba da gagarumar gudunmawa a fannonin kiwan lafiya da Asibitocin dake fadin jihar nan da suka hadar da Asibitin Murtala da Asibitin Abdullahi wase da Asibitin Dala da sauran Asibitocin dake jihar kano.
Haka zalika,Aminu Abdullahi Bayero, ya yi kira ga Gwamnatin jihar kano da Kungiyoyin tallafawa Alumma da masu hannu da shuni da su kasance masu taimakawa marasa lafiya da masu bukata ta musamman da masu karamin karfi duba da halin matsin Rayuwa da Alummar kasar nan suka tsinci Kansu a ciki.
Daga karshe Shugaban Kungiyar Matasan Unguwar ta Dorayi ya godewa Shugaban Gidauniyar Lafiya Sak, Dr. Zaharaddeen Adam Zakirai,bisa wannan gagarumar gudunmawa da yake yi ta fannoni da dama domin taimakawa marasa lafiya da masu karamin karfi domin inganta rayuwarsu yadda ya kamata.












