DAGA HASSAN UMAR GWAMMAJA
Kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika ECOWAS ta yanke shawarar dage wasu takunkumin da ta kakabawa jamhuriyar Nijar da Mali da kuma Guinea.
An dauki wannan kuduri ne a wani babban taro na musamman kan harkokin zaman lafiya, siyasa da tsaro a yankin ECOWAS da aka gudanar a Abuja ranar Asabar nan.












