Rundunar sojin ƙasa ta Najeriya ta shirya za ta saki sama da mutane 200 da aka wanke daga zargin alaƙa da ƙungiyar ƴan ta’addan Boko Haram.
Kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito, sojoji sun kama waɗannan mutanen ne a lokacin da ayyukan ƴan tada kayar baya ke cin kasuwa a Arewa maso Gabas.
Binciken ya nuna cewa za a mika su ga gwamnatin jihar Borno domin su koma cikin al’umma yadda ya kamata.
Za a gudanar da taron sakin mutanen a barikin sojojin Giwa da ke Maiduguri, babban birnin jihar Borno a safiyar ranar Talata.
“Jami’an tsaro sun wanke kimanin mutane 200 daga zargin alaƙa da Boko Haram da duk wani laifi kuma za a miƙa su ga gwamnatin Borno domin sake maida su cikin al’umma.
“An shirya bikin mika mutanen da aka wanke daga zargin a safiyar yau (Talata, 26 ga watan Maris) da karfe 10:00 na safe a barikin Giwa,” in ji wata majiya.
Majiyar ta ce kwamishinar harkokin mata ta Borno, Zuwaira Gambo da takwaranta na yada labarai da tsaron cikin gida Farfesa Tar Umar za su karbi wadanda aka sako a madadin gwamnatin jihar.











