Hukumar dake kare hakkin masu amfani da kayayyaki ta tarayya, ta rufe babban kantin Sahad da ke Garki, a babban birnin tarayyar, Abuja kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.
An zargi shugabannin kantin da yin almundahana ta hanyar cajar kwastomomi kudin da suka haura wanda aka lika a jikin kaya.
Mukaddashin mataimakin shugaban hukumar FCCPC, Adamu Ahmed Abdullahi ne ya jagoranci sumamen.
Cikakken rahoton na nan tafe












