Jam’iyyar APC reshen jihar Kano ta yi fatali da gayyatar da hukumar yaƙi da cin hanci ta tura wa tsohon gwamna Abdullahi Ganduje
A wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun shugaban APC da sakatare, jam’iyyar ta buƙaci Ganduje kar ya amsa gayyatar
Ta ƙara da cewa gwamnatin Kano ta dawo da batun bidiyon dalar ne domin su bata wa Ganduje suna
Idan baku manta ba a cikin shirin Channels tv, shugaban hukumar, Muhuyi Magaji Rimingado, ya ce sun gayyaci Ganduje domin ya yi ƙarin haske kan bidiyon dala a mako mai zuwa.
Amma da suke martani kan lamarin, shugaban APC na Kano, Abdullahi Abbas da sakararen jam’iyya na jiha, Alhaji Zakari Sarina, sun zargi gwamnatin Kano da ƙulla wa Ganduje makirci.












