AKSAMMEDIA-KANO– Rundunar sojin Iran ta sanar da cewa ta dakile wani yunkuri da Amurka ta yi na ceto wani matukin jirgi da ya fadi, inda aka lalata jiragen sama da dama ciki har da jiragen helikwafta na Black Hawk da kuma jirgin daukar kaya na soja a wani samame da aka kai a kudancin Isfahan.
Mai magana da yawun hedikwatar Khatam al-Anbia Central Headquarters ne ya bayyana hakan a ranar Lahadi, 5 ga Afrilu, inda ya ce rundunar sojin Iran ta lalata wasu jiragen saman Amurka a kudancin Isfahan, tare da dakile wani yunkuri na cetar wani matukin jirgin yaki na Amurka da ya fadi.
Ya ce lamarin ya biyo bayan yunkurin da sojojin Amurka suka yi na kutsawa cikin tsakiyar Iran domin fitar da matukin jirgin.
Kakakin ya kara da cewa wani hadin gwiwa tsakanin rundunar sararin samaniya da ta kasa, tare da dakarun sa-kai na Basij da jami’an tsaro, ya yi nasarar dakile hare-haren jiragen da ke shigowa tare da tarwatsa su.
Ya bayyana cewa an lalata jiragen makiya da dama, yana mai cewa wannan wani sabon koma baya ne ga Amurka, inda ya kwatanta da gazawar Operation Eagle Claw a watan Afrilu na shekarar 1980.
Har ila yau, ya ce shugaban Amurka Donald Trump ya yi kokarin rage girman lamarin ta hanyar wallafa sako a shafukan sada zumunta yana mai cewa an gudanar da wani aiki na musamman domin ceto matukin jirgin.
Mai magana da yawun ya jaddada cewa kokarin makiyan ya ci tura ne sakamakon hadin kai da saurin daukar mataki na rundunar Iran, ciki har da Islamic Revolutionary Guard Corps, rundunar soji, dakarun Basij da kuma jami’an ‘yan sanda.
Ya kara da cewa jiragen da aka lalata sun hada da helikwafta biyu na Black Hawk da kuma jirgin daukar kaya na soja nau’in C-130, wadanda aka harba kuma suka kama da wuta a kudancin Isfahan.












