• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Yadda hare-haren Boko Haram ya mayar da wasu gurare kufai a jihar Borno

aksam by aksam
May 14, 2025
Reading Time: 3 mins read
0
Home LABARAI
ADVERTISEMENT
474
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Duk da cewa an daɗe ana ganin cewa dakarun Najeriya tare da hadin gwiwar ƙasashen makwabta sun raunana ƙungiyar Boko Haram, hare-haren da ƙungiyar ke kai wa a Najeriya sun ƙaru sosai a cikin shekaru uku da suka gabata.

A binciken da kafar yaɗa labarai ta BBC ta yi bisa bayanai daga cibiyar SBM Intelligence kamfani da ke tattara bayanan tsaro a nahiyar Afirka – hare-haren da ake danganta wa Boko Haram sun ƙaru daga 105 a shekarar 2022, zuwa 147 a sekarar 2023, sannan suka kai 191 a shekarar 2024.

RelatedPosts

Sarkin Zurmi Ya Rasu Bayan Shekaru Biyar A Kan Sarauta

Kano State Govt ends 50 year BUK/Rimin zakara Land Dispute

Yaki da harkar Daba a Jihar Kano

A shekarar 2025 kuma, harin farko da Boko Haram ɗin suka kai ya faru ne a ranar 4 ga watan Janairu, lokacin da Boko Haram ta yi wa sojojin Najeriya kwanton ɓauna a kauyen Sabon Gari, inda suka kashe sojoji shida. Kwana tara bayan haka, a ranar 13 ga Janairu, ƙungiyar ta sake kai wani hari a ƙauyen Dumba kusa da Baga, inda ta kashe manoma da masunta 40.

Tun daga wannan lokaci, ƙungiyar Boko Haram ta ci gaba da kai hare-hare a kowane wata a wannan shekara, tare da ƙaruwar yawan su. Wannan yana nuna wata matsala ta sake dawowar tashin hankali, musamman a yankunan karkara da kuma gefen birane.

ranar 8 ga watan Afrilun 2025, gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya bayyana damuwa game da dawowar hare-haren Boko Haram da kuma ƙaruwar sace-sacen mutane. Ya ce ƙungiyar na ƙoƙarin dawowa inda sau da dama ta kai hari kan sansanonin sojoji da kashe fararen hula.

“Kashe fararen hula da jami’an tsaro abin damuwa ne matuka, kuma yana nuna koma baya mai girma ga jihar Borno da yankin arewa maso gabas gaba ɗaya,” in ji Zulum.

Rahotanni daga jihohin Borno da Yobe na nuna cewa ƙaruwar hare-haren ƙungiyar na nuni da cewa ba a ci galaba ba yadda ake tunani wajen kawar da ƙungiyar.

“Abin da muka gani ba ƙaramin abu bane, yana nuna cewa mutane na fara rasa fata da karfin gwiwa. Kowa na cikin tsoro, zuciya cike da fargaba, mutane na kokarin daidaita tunaninsu,” in ji Aliyu Harande, wani mazaunin garin Mafa, cikin hirarsa da BBC bayan harin da aka kai a shekarar da ta gabata.

“Ga mu da muka ɗauka cewa hare-haren Boko Haram ɗin sun lafa, wannan harin ya bayyana mana cewa ba haka bane, harin ya nuna mana cewa suna sake taruwa” in ji shi.

Zanna Umara, wani jami’i a ƙaramar hukumar Tarmuwa, ya shaida wa BBC cewa: “Ba ma fatan dawowarsu, amma ganin irin harin da suka kai a Mafa, yana nuna kamar da gaske suna kokarin dawowa ne.”

Dr. Kabir Adamu, shugaban kamfanin tsaro na Beacon Security and Intelligence Limited kuma masani a fannin tsaro ya ce ƙaruwar hare-haren da ake gani a baya-bayan nan na da nasaba da wasu dalilai.

Na farko, in ji shi, shi ne sakin wani umarni daga kungiyar ISIS da ke buƙatar duka rassanta su kara yawan hare-hare, kuma an ga ƙungiyoyi daban-daban suna amsa wannan kiran.

Abu na biyu da Dr. Adamu ya danganta karuwar hare-haren Boko haram da shi shi ne wani yanayi na lokaci.

“Kafin lokacin damina, wadannan ƙungiyoyi sukan ƙara ƙaimi wajen kai hare-hare, domin sun san ayyukan soji kan ragu a lokacin saboda wahalar hanya da ƙarancin gani,” in ji shi.

Ya kara da bayyana cewa rashin zaman lafiya a yankin Sahel na daya daga cikin manyan dalilai. “Tashe-tashen hankula a Sahel, musamman a kasashen Chadi da Nijar da Burkina Faso, sun raunana tsaron iyakoki, hakan ya bai wa waɗannan ƙungiyoyi damar motsawa da ɗaukar sabbin mambobi da samun tallafi cikin sauki,” in ji masanin.

Dr. Adamu ya kuma ce sauye-sauyen da aka yi a tsarin rundunar sojin Najeriya sun taimaka wa Boko Haram ƙara ƙaimi wajen kai hare-hare musamman yadda aka mayar da kayan yaƙi da sojoji daga arewa maso gabas zuwa arewa maso yamma domin sabbin hare-hare.

Sai dai gwamnatin Najeriya ta ce karuwar hare-haren Boko Haram yana da nasaba da yawaitar ayyukan ‘yan tada ƙayar baya a ƙasashen makwabta.

Share190Tweet119SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Gwamnan Kano Abba Kabeer Yusuf Ya Raba Kayayyakin Harkokin Ilimi Ga Makarantun Jihar

Next Post

Cikin Yan majalissun jahar kano goma Sha shida na yankin kano ta kudu,daya ne yabi kawu sumaila: Hon Garba Umar Durbunde

aksam

aksam

RelatedPosts

Sarkin Zurmi Ya Rasu Bayan Shekaru Biyar A Kan Sarauta
LABARAI

Sarkin Zurmi Ya Rasu Bayan Shekaru Biyar A Kan Sarauta

by Khadija Maitaya
September 1, 2026
Kano State Govt ends 50 year BUK/Rimin zakara Land Dispute
LABARAI

Kano State Govt ends 50 year BUK/Rimin zakara Land Dispute

by Khadija Maitaya
August 31, 2026
Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro
LABARAI

Yaki da harkar Daba a Jihar Kano

by Khadija Maitaya
August 31, 2026
Babban Malami Ya Kalubalanci Gwamnoni da ’Yan Majalisa Bisa Rufe Cibiyoyi 10 Na Yin Fasfo
LABARAI

Babban Malami Ya Kalubalanci Gwamnoni da ’Yan Majalisa Bisa Rufe Cibiyoyi 10 Na Yin Fasfo

by Khadija Maitaya
August 30, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Yanzu-yanzu Tinubu na gudanar da taro da shugabannin tsaro na Najeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Shirinta Na Siyyar Da Buhun Shinkafa Akan Naira Dubu 40,000

August 8, 2024
Rashin tsaro da tsadar takin zamani ya haifar da durkushewar harkokin kasuwanci

Rashin tsaro da tsadar takin zamani ya haifar da durkushewar harkokin kasuwanci

October 30, 2025
ADVERTISEMENT

Trending.

Masu Siye Da Siyar Da Filaye A  R/zakara Sunkoka Da Aibantasu Da Gwamnatin Kano Keyi.

Masu Siye Da Siyar Da Filaye A  R/zakara Sunkoka Da Aibantasu Da Gwamnatin Kano Keyi.

August 26, 2026
Cristiano Ronaldo Ya Auri Georgina Rodríguez

Cristiano Ronaldo Ya Auri Georgina Rodríguez

August 12, 2026
Wani Kauran Mata Ya Jikkata Wata Dattijuwa Bayan Ta Hana Shi Shiga Gurin Da Bai kamata Ba

Wani Kauran Mata Ya Jikkata Wata Dattijuwa Bayan Ta Hana Shi Shiga Gurin Da Bai kamata Ba

August 29, 2026
IPMAN Ta Nemi Dangote Ya Fara Kai Man Fetur Kai Tsaye zuwa Arewacin Najeriya

IPMAN Ta Nemi Dangote Ya Fara Kai Man Fetur Kai Tsaye zuwa Arewacin Najeriya

August 23, 2026
Masu Zuba Jari 40+ daga Masar na Sha’awar Zuba Jari A Najeriya

Masu Zuba Jari 40+ daga Masar na Sha’awar Zuba Jari A Najeriya

August 23, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media