A ya yi hukuncin da ta yanke, kotun ta amince da matsayar kotun sauraron ƙorafin zaɓen jihar Kano, wadda ta ce ba a bi ƙa’ida ba wajen tsayar da Abba Kabir takara, saboda haka bai cancanci tsayawa takara a zaɓen na gwamna ba.
A ranar 20 ga watan Satumba ne kotun sauraron ƙorafin zaɓe ta jihar Kano ta ce Gawuna ne ya lashe zaɓen wanda aka gudanar a watan Maris.
Kotun ta ce ba za a sanya ƙuri’u 165,663 da aka kaɗa wa Abba Kabir cikin lissafi ba kasancewar babu sa hannu ko tambarin kan sarki na hukumar zaɓe a jikinsu.
Hakan ne ya sanya aka zabge ƙuri’in Abba zuwa 853,939, yayin da shi kuma Gawuna ke da ƙuri’u 890,705.
Sai dai Abba Kabir ya yi watsi da hukuncin inda ya garzaya kotun ɗaukaka ƙara.
Ya bayyana sakamakon kotun sauraron ƙorafin zaɓen a matsayin “kuskure” kuma maras “adalci”.












