• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Yadda abun da ke faruwa a Gaza ya saka wani ba Amurke da matarsa musulunta

aksam by aksam
March 13, 2024
Reading Time: 3 mins read
0
Home LABARAI
ADVERTISEMENT
467
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Marubuci kuma ɗan gwagwarmaya Jeffery Shaun King da matarsa Rai King sun musulunta a ranar farko ta watan Ramadan.

Su biyun sun karɓi shahada a ranar Litinin inda aka watsa kai tsaye a shafin Instagram, ƙarƙashin jagorancin abokin King na sama da shekaru 10 – malamin Musuluncin nan na Amurka Omar Suleiman.

RelatedPosts

Sarkin Zurmi Ya Rasu Bayan Shekaru Biyar A Kan Sarauta

Kano State Govt ends 50 year BUK/Rimin zakara Land Dispute

Yaki da harkar Daba a Jihar Kano

King mai shekara 44 sanye da shigar Falasɗinawa ta jallabiya da hirami, yayin da yake jawabi ga taron, ya ce ya yanke shawarar shiga Musulunci ne bayan “wata shida da suka gabata na wahala da raɗaɗi da tashin hankalin da muka gani a Gaza”.

“Abin ya taɓa ni sosai ganin mutane a yanzu a cikin mafi haɗari da wuri mai ban tsoro a duniya ba sa iya kallon komai sai tarkace da ragowar danginsu, kuma har yanzu suna ganin ma’ana da manufa a rayuwa.”

“Ba ni kaɗai imaninsu da miƙa wuyansu ga Musulunci ya buɗe wa zuciya ba, ya buɗe zuciyoyin miliyoyin mutane a faɗin duniya,” a cewar King.

King ya kasance mai yawan bayyana ra’ayi da nuna goyon bayansa ga Falasɗinu a kan yaƙin da take yi da Isra’ila a Gaza da aka yi wa ƙawanya, wanda ya kashe aƙalla mutum 31,112, mafi yawansu yara da mata, sannan zuwa yanzu mutum 72,760 sun jikkata.

Tun ranar 7 ga watan Oktoba, King yake wallafa saƙonni a shafukan sada zumunta da ke nuna yadda ake lalata Gaza, tare da yin kira da a kawo ƙarshen hare-haren Isra’ila.

King har sai da ya yi ikirarin cewa ya yi aiki da ƙungiyar Hamas don a saki Amurkawa biyu da aka yi garkuwa da su: Natalie Raanan mai shekara 17 da mahaifiyarta Judith Tai Raanan mai shekara 59. Ikirarin da iyalansu suka musanta.

A martanin da ya yi na goyon bayan Falasɗinu da yake yi, King ya ce Instagram sun rufe shafinsa mai yawan mabiya sama da miliyan shida a watan Disamba. Har yanzu ba a san dalilin da ya sa kamfanin Meta suka rufe shafin King ba.

To amma wane ne Shaun King kuma me ya sa yake fafutukar kare Falasɗinawa?

Ya sha fama da wariya da kalaman tsana

Daga yadda gungun matasa suka taɓa yunƙurin taka shi da motar ɗaukar kaya a makaranta zuwa yi masa tiyatar ƙashin baya saboda harin da ɓata-gari da ake kira “rednecks” suka kai masa, King yana yawan magana kan nuna wariyar launin fata da ya fuskanta a lokacin da yake yaro a matsayinsa na ɗan wata ƙabilar daban da ya girma a jihar Kentucky ta Amurka.

Bayan wani hari da aka taɓa kai masa, King ya ce wata ziyara da babban abokinsa na makarantar sakandare da babansa, wanda fasto ne, suka kai masa, ta sa shi fara tunanin samun abin yi a addini.

King ya ce ya girma a matsayin maraya kuma “ziyarar da wannan mutum ke kai mini ta sa na ji ina son zama kamar sa.”

Bayan kammala karatunsa, King ya ɗan yi koyarwa a makarantar sakandare da kuma fannin shari’a, kafin daga baya ya zama fasto a wata coci a Georgia.

A shekarar 2008 ne ya kafa coci a Atlanta da ake kira Courageous Church, kuma yana yawan amfani da shafukan sada zumunta wajen shigar da mutane addinin, har ma ake yi masa laƙabi da “Faston Facebook.”

Sai dai kuma, bayan shekaru huɗu kawai sai ya yi murabus daga coci saboda “damuwa da gajiya.”

Fafutuka don kare hakkin jama’a

Duk tsawon lokacin, yana yin la’akari da abubuwan da ilimin da ya koya da suka shafi laifukan nuna ƙiyayya, King ya sadaukar da rayuwarsa don inganta al’amuran zamantakewa, musamman a fafutukar tabbatar da cewa rayuwar baƙaƙen fata na da muhimmanci, wato “Black Lives Matter Movement.”

Ya yi hakan ne ta hanyar rubuce-rubucen da suka mayar da hankali kan ‘yancin ɗan’adam da ƙabilanci da zaluncin ‘yan sanda da ɗaure jama’a da kuma rashin ɗa’a.

Yana yawan rubuce-rubuce a kafafen watsa labarai kamar su Daily Kos da the New York Daily News da kuma The Young Turks.

Share187Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Yadda mayakan IPOB suka fara hada jiragen yaki maras matuki

Next Post

Tinubu ya bayar da umarnin buɗe iyakokin Najeriya da Nijar

aksam

aksam

RelatedPosts

Sarkin Zurmi Ya Rasu Bayan Shekaru Biyar A Kan Sarauta
LABARAI

Sarkin Zurmi Ya Rasu Bayan Shekaru Biyar A Kan Sarauta

by Khadija Maitaya
September 1, 2026
Kano State Govt ends 50 year BUK/Rimin zakara Land Dispute
LABARAI

Kano State Govt ends 50 year BUK/Rimin zakara Land Dispute

by Khadija Maitaya
August 31, 2026
Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro
LABARAI

Yaki da harkar Daba a Jihar Kano

by Khadija Maitaya
August 31, 2026
Babban Malami Ya Kalubalanci Gwamnoni da ’Yan Majalisa Bisa Rufe Cibiyoyi 10 Na Yin Fasfo
LABARAI

Babban Malami Ya Kalubalanci Gwamnoni da ’Yan Majalisa Bisa Rufe Cibiyoyi 10 Na Yin Fasfo

by Khadija Maitaya
August 30, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Vigilantes Kill Notorious Bandit Leader Kachalla Sani Yellow in Zamfara

Vigilantes Kill Notorious Bandit Leader Kachalla Sani Yellow in Zamfara

July 12, 2026
Kungiyar masu sana’ar wayoyin hanu ta Kano zata haɗa hannu da  Gwamnatin Kano kan Muhimmin al’amari

Kungiyar masu sana’ar wayoyin hanu ta Kano zata haɗa hannu da Gwamnatin Kano kan Muhimmin al’amari

September 19, 2025
ADVERTISEMENT

Trending.

Masu Siye Da Siyar Da Filaye A  R/zakara Sunkoka Da Aibantasu Da Gwamnatin Kano Keyi.

Masu Siye Da Siyar Da Filaye A  R/zakara Sunkoka Da Aibantasu Da Gwamnatin Kano Keyi.

August 26, 2026
Cristiano Ronaldo Ya Auri Georgina Rodríguez

Cristiano Ronaldo Ya Auri Georgina Rodríguez

August 12, 2026
Wani Kauran Mata Ya Jikkata Wata Dattijuwa Bayan Ta Hana Shi Shiga Gurin Da Bai kamata Ba

Wani Kauran Mata Ya Jikkata Wata Dattijuwa Bayan Ta Hana Shi Shiga Gurin Da Bai kamata Ba

August 29, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Matar Aure Hukunci Bayan Samunta Da Watsa Tafasasshen Ruwa Ga Kishiyarta

Kotu Ta Yanke Wa Matar Aure Hukunci Bayan Samunta Da Watsa Tafasasshen Ruwa Ga Kishiyarta

August 7, 2026
Iran Ta Kakkabo Wasu Manyan Jiragen Yaƙi Na Amurka

Iran Ta Kakkabo Wasu Manyan Jiragen Yaƙi Na Amurka

August 14, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media