Firaministan Birtaniya Keir Starmer ya zayyana wasu matakai da za a bi domin tsaurara dokokin shiga da zama a ƙasar, da zimmar rage kwarorowar baƙi masu zuwa zama da karatu da neman aiki.
Daga cikin matakan akwai gwajin Ingilishi ga dukkan masu neman izini shiga ƙasar da kuma tsawaita lokacin da ake ɗauka a ƙasar kafin samun izinin zama na dindindin.
Firaministan yana kuma so a rage ɗaukar ma’aikatan jinya daga ƙasashen ƙetare, matakin da zai taimaaka wajen rage yawan ƴan ƙsashen waje da ake ɗauki aiki a ƙasar ta sahihiyar hanya.
Sai dai bai ce komai ba game da masu shiga ƙasar ta ɓarauniyar hanya, kamar masu shiga ta teku.
Adadin baƙin da suka shiga ƙasar a shekarar 2024 sun kai 728,000 zuwa watan Yunin shekarar.
Hukumomin ƙasar za su fitar da gamsasshen bayani mai ɗauke da sababbin tsauraran matakan, waɗanda za su ƙunshi na mallakar izinin karatu da aiki a Birtaniya.
Sakataren harkokin baƙi na Birtaniya Yvette Cooper ta bayyana wa BBC cewa lokaci ya yi da za su rage ɗaukar ma’aikatan jinya daga ƙasashen waje.
Ta ce wannan matakin zai taimaka wajen rage kusan mutum 50,000 waɗanda ba ƙwararru ba ne sosai da suke shiga ƙasar daga ƙasashen ƙetare a duk shekara.
Firaministan ya ce sababbin matakan za su taimaka wajen “sake mallake bakin iyakokin ƙasarmu.”
Idan aka ɗabba sabbin matakan nan da gwamnatin ƙasar za ta ɗauka, ƴan ƙasashenmutane daga ƙasashen Najeriya da Pakistan da Sri Lanka za su fuskanci ƙalubale wajen samun izinin shiga ƙasar Birtaniya domin karatu.
Starmer ya ce Birtaniya za ta riƙa neman waɗanda suka fi ƙwarewa ne a duniya wajen ɗaukar aiki, sannan za su bincika me ya sa wani ɓangaren aikin ƙasar ya fi mayar da hanakali kan “neman sauƙi wajen ɗaukar aiki.”
Firaministan ya ce sabbin matakan za su fayyace komai da komai game da tsare-tsaren shige da fice a ƙasar – iyali da karatu da aiki.
“Zan tabbatar da matakan nan saboda za su tabbatar da adalci, kuma abin da ya dace ke nan,” in ji Starmer a wani taron manema labarai.
Ya ce bai kamata a riƙa mayar da hankali kan neman sauƙi wajen ɗaukar ma’aikata ba, maimakon mayar da hankali kan horar da matasan ƙasar.
Starmer ya ƙara da cewa baƙin da suke shigowa ƙasar a gwamnatin baya sun kai kusan miliyan 1 a shekarar 2023, wanda shi ne adadi mafi yawa.
Ya ce adadin baƙin ya kai adadin mutanen birnin Birmingham baki ɗaya, wanda kuma shi ne birni na biyu mafi girma a Birtaniya.
“Wannan ba ci gaba ba ne, kasada ce. Ba zai yiwu a ce da kuskure hakan ya faru ba, wannan ganganci aka yi












