Shugaban Amurka Donald Trump ya ce lamari ne da ya rataya a wuyan Shugaban ƙasar China, Xi Jinping, kan ko China za ta karɓe iko da Taiwan.
A cewarsa, Xi Jinping na kallon Taiwan a matsayin wani ɓangare na ƙasar China, kuma ya ce shawarar abin da zai yi game da hakan tana hannunsa ne. Trump ya bayyana haka ne a wata hira da jaridar The New York Times.
Sai dai Trump ya jaddada cewa ya sanar da Shugaban China cewa ba zai ji daɗi ba ko kaɗan idan har China ta ɗauki matakin ƙwace Taiwan. Ya ce ya nuna rashin amincewarsa da duk wani mataki da zai kai ga mamaye ko karɓe ikon tsibirin.











