Wasu gungun ‘yan bindiga sun kashe jami’an ‘yan sanda hudu da fararen hula biyu a wani sabon hari da suka kai jihar Katsina
An ruwaito cewa ‘yan bindigar sun farmaki sansanin da jami’an tsaron ke zama a garin Garagi, kauyen Yartsamiyar Jino
Mazauna yankin da suka zanta da manema labarai sun ce ‘yan ta’addan sun yi awon gaba da bindigogin ‘yan sandan da aka kashe












